• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, January 22, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNKASA MALUMFASHI DA KEWAYE (6)

RAHOTON MUSAMMAN

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
August 14, 2025
in Gizago
0
TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNKASA MALUMFASHI DA KEWAYE (6)

A dama, Injiniya Muntari Sagir yana amsar Kambin Girmamawa daga Shugaban Ƙaramar Hukumar Malumfashi, Mukhtar Abdullahi City, a zauren taron

47
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNKASA MALUMFASHI DA KEWAYE (6)

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

My 83rd Birthday and the Kindred Spirit

Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya

January 19, 2026
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (9)

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (9)

January 17, 2026
Injiniya Muntari Sagir Malumfashi, yayin gabatar da jawabinsa a wurin taron

 

                            •••••••

Kamar yadda muka bayyana a rahoto kashi na 5, a yau za mu karkata ne zuwa ga muhimman mutanen da aka karrama a yayin wannan taro. Za mu fara da Injiniya Muntari Sagir, wanda shi ma ya gabatar da jawabi, a yayin da aka karrama shi.

√ Wane Ne Injiniya Muntari Sagir?
Wannan bawan Allah, ɗaya ne daga cikin matasan attajiran da Allah ya albarkaci Ƙaramar Hukumar Malumfashi da kewaye da su. Mutum ne shi da Allah ya ba shi wasu keɓaɓɓun halaye guda biyar.

Waɗannan halaye su ne, “Kishin Al’umma.” Ga dukkan masu bibiyar al’amuransa a Malumfashi, zai tabbatar da wannan halayya tasa. Na biyu, mutum ne shi mai “Kawaici.” Wannan halayya ce ta sanya wasu ma da ba su yi mu’amala da shi ba suke zaton cewa Muntari Sagir mai girman kai ne. Kuma alhali ba haka al’amarin yake ba, domin kuwa halayyarsa ta kawaici ce ta sanya ba ya shiga harkar da ba ta shafe shi ba, ba ya da yawan magana ko surutu.

A dama, Injiniya Muntari Sagir ne, yake taya murna ga Malam Haruna Musa Rigoji ne, jim kaɗan bayan da Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari ya karrama shi, a 2022

Halayyarsa ta uku, ita ce “Sanin Ya Kamata.” Hakan ke nufin cewa shi mutum ne mai natsuwa da tsara duk abin da yake son aiwatarwa. Na huɗu, Injiniya mutum ne “Mai Kyauta.” Halayyarsa ta biyar, ita ce “Zumunci.” ‘Yan uwa, abokansa da dukkan waɗanda suka jiɓance shi, su ne manyan shaidun da za su tabbatar da wannan babbar halayya tasa.

√ Jawabinsa A Taron Facebook:
Injiniya Muntari Sagir na ɗaya daga cikin zaratan mutanen da aka karrama a wannan muhimmin taro da aka gudanar a Malumfashi. A lokacin da aka gabatar da shi domin ya yi jawabi. Bai yi ƙasa a gwiwa ba.

Injiniya ya yi godiya, kamar kuma yadda ya yaba wa matasan da suka shirya wannan taro. Ya yi wa al’ummar Malumfashi albiahir da cewa, kamfaninsa zai gina katafaren zauren shirya taro na zamani (Event Centre) a Malumfashi. Kamar yadda ya ce, “in sha Allahu, a taron Malumfashi Facebook Connect na baɗi 2026, a cikin wannan sabon zauren da zan gina za a gudanar da shi.”

A jawabin nasa, a matsayinsa na matashi, wanda ya damu da ci gaban matasa da sauran al’ummar Malumfashi da kewaye, Injiniya ya ba matasa shawarwari game da rayuwa. Ya ce ya kamata matasa su daina zaman banza, su daina bari zuciyarsu tana mutuwa, su riƙa nemab aiki ko sana’a komai ƙankantarta. Ya ce “ba daidai ba ne yadda wasu matasa suka zama masu rashin kunya da wulaƙanta manya. Idan Allah ya azurta wani ko ya ba shi mulki, ba ƙarfinsa ko dubararsa ba ce. Maimakon ku riƙa nuna ƙyashi da hassada, ku tashi ku nema wurin Allah. Ku ma zai iya ba ku naku, domin shi ne ke bayarwa ga wanda ya so.”

Injiniya Muntari, a zauren taron

Haka kuma ya yi gargaɗi na musamman ga wasu matasa da ke yin shaye-shaye kuma suke yi wa al’umma sace-sace da ɓarnata masu dukiya. Ya ce su shiga taitayinsu, domin akwai hukuma kuma akwai hukunci ga duk wanda ya fitsare ƙafarsa, ya shiga cikin irin wannan mummunar ɗabi’a.

√ Wasu Muhimman Bayanai:
A wata ganawa ta musamman da na yi da Injiniya Muntari Sagir, na tambaye shi game da wasu halaye nasa, musamman ayyukan tallafa wa al’umma da yake yi. Sai ya bayyana cewa: “A matsayina na Musulmi, na yi imani da Allah, cewa kyautatawa da tallafa wa al’umma abubuwa ne masu kyau, waɗanda Allah da manzonsa suke so. Don haka Allah ya hore mani, babu dalilin da zai sanya in riƙe hannu, in ƙi taimakon al’umma, alhali suna da buƙata.”

Ya ƙara da cewa, “idan na ga wani cikin matsala, kamar rashin lafiya ko wani rashi, nakan yi tunanin cewa idan ni ne nake cikin irin wannan jarabawar, yaya zan ji? Don haka ba na jin daɗin in ga na kasa taimako mai neman taimako. Kuma abin ikon Allah, ina ganin buɗi daga wurin Allah.”

Ko Injiniya yana da sha’awar tsayawa takarar wani muƙami a siyasa? Tambayar da na yi masa ke nan, inda shi kuma ya amsa da cewa: “A gaskiya a yau shugabanci ya koma wani irin abu, inda ake faɗin al’amura da baki, aikatawa ya gagara. Duk yadda shugaba a mulkin siyasa ya so ya kamanta gaskiya da adalci, idan bai samu mataimaka na gaske ba, ba zai iya aikata wani abin kirki ba. Don haka ba ya cikin tsarina, ba zan fito wata takarar kujerar siyasa ba. Amma za mu ci gaba da taimakawa ta hanyar da Allah ya ba mu, ta hanyar sana’armu.”

√ Ayyukan Jin Ƙai Da Raya Al’umma:
Kamar yadda muka tsakura a gabatarwa, cewa Injiniya Muntari Sagir mutum ne mai sanin ya kamata, mai kishin al’umma kuma mai kyauta, to hakan ta tabbata a rayuwarsa. Wannan dalili na daga cikin abin da ya sanya aka karrama shi da KAMBIN GIRMAMAWA a wannan taro.

Daga hagu: Injiniya Muntari Sagir da Alhaji Jibrin Sama’ila (Jinsin) da sauran manyan baƙi a zauren taron

Kaɗan daga ayyukan da yake wa al’umma sun haɗa da ginawa da yaran masallatai. Ginawa da gyaran asibiti da ɗakunan shan magani. Ginawa da gyaran makarantun Islamiyya da na boko. Yana ginawa da gyaran kwalbatoci. Yana tallafa wa ɗalibai da kuɗin makaranta ko na jarabawar WAEC, NECO, JAMB da sauransui. Yana tallafa wa marasa lafiya da kuɗin magani, yana gina rijiyoyin burtsatse.

Wannan shi ne Injiniya Muntari Sagir Malumfashi. Idan Allah ya kai mu rahoto na 7, za mu duba rayuwar Alhaji Jibrin Sama’ila (Jibson), wanda shi ma aka karrama a wannan taro.
______________

Previous Post

KTSTA: HARKAR SUFURI A HANNUN GWANI (3)

Next Post

JONATHAN – KWANKWASO: Sabon Lissafin 2027

Related Posts

My 83rd Birthday and the Kindred Spirit
Gizago

Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya

January 19, 2026
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (9)
Gizago

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (9)

January 17, 2026
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (8)
Gizago

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (8)

January 13, 2026
Next Post
JONATHAN – KWANKWASO: Sabon Lissafin 2027

JONATHAN - KWANKWASO: Sabon Lissafin 2027

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Wasu Muhimman Darussa Daga Zantuttukan Bukar Usman

Wasu Muhimman Darussa Daga Zantuttukan Bukar Usman

July 24, 2023
Har Yanzu Akwai Cutar AIDS Kuma Za Mu Taru Mu Yaƙe Ta Da Gaske – Dokta Bala Nuhu

Har Yanzu Akwai Cutar AIDS Kuma Za Mu Taru Mu Yaƙe Ta Da Gaske – Dokta Bala Nuhu

July 6, 2023
Nigerian Army Bursts Gun Manufacturing Syndicate

Nigerian Army Bursts Gun Manufacturing Syndicate

September 24, 2023
BIU: A Visit to a City on a Plateau (5)

BIU: A Visit to a City on a Plateau (5)

February 9, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)
  • Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya
  • Nazari, Tsokaci Da Sharhin Littafin Tarkon Mut’a

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)

January 21, 2026
My 83rd Birthday and the Kindred Spirit

Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya

January 19, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.