KE YARINYA: ANYA KUWA YANA SON KI DA GASKE?

•••
Ya kalle ta guƙi, idanuwansa a cikin nata ya ce: “Ga ki kyakkyawa, son kowa ƙin wanda ya rasa. Ga ki da fasali da kyan diri, ga ƙuruciya, wacce kowane ɗa namiji ya kalle ki zai ji e, yane-yane!
“Kuma ba ki rasa manema ba fa, domin ga su nan birjik! A kullum kika fita sai an samu masu tayawa. Mazaje na gaske, attajirai, ‘yan siyasa da manyan ma’aikatan gwamnati; waɗanda daɓensu ya gama jin makuba.”
‘Yar Auta dai har yanzu tana sauraren shi ba tare da ta ce uffan ba. Shi kuwa bai tsaya ba, ya ci gaba da maganarsa. “A cikin maneman naki, akwai wani guda ɗaya tamkar da dubu, wanda ke share maki kowane irin kuka – madamar kuɗi na maganinsa.
“Kin fi ƙarfin motar shiga ta zamani, komai tsadar ta. Kin fi ƙarfin muhalli mai kyau mai tsada, mai ƙaye, cike da kayan alatu na zamani.
“Wayar zamani komai tsadar ta, kina cikin sahun farko na masu mallakar ta.
“Kin fi ƙarfin kuɗin kashe galarin gabanki. Kina kyauta da Dala ba Naira ba. Kin maida Saudiya, Dubai da sauran manyan biranen duniya kamar ƙasashen haihuwarki.

“A taƙaice dai, a duk rayuwarki, babu abin da kika rasa sai abu ɗaya – Aure! Kin shaida mani cewa, a duk lokacin da kika yi wa maneminki maganar aure, ba ya so. Ɓata rai yake yi. A taƙaice ma, kwanakin baya da kika sake tada masa da batun AURE, fitowa ya yi hoha, ya shaida maki cewa: “Ni fa ina son ki ne kawai amma ba da AURE ba! Don haka, kada ki ƙara yi mani maganar aure a sha’anin rayuwarmu!”
‘Yar Auta ta ja dogon numfashi, fuskarta a murtuke kamar hadarin da ke shirin zubar ruwa; ta kalli mutumin da take kira da Yaya amma ta kasa furta komai. Ta sake duƙar da kai ƙasa, wani hawaye mai ɗumi ya fara biyar kumatunta.
“Ke nan lokaci ya yi da ya kamata ki nazarci rayuwarki.” Yayan nata ya ci gaba da magana. “Ki yi karatun-ta-natsu, tun kafin lokaci ya gama ƙure maki. Ki tambayi kanki, shin me ya sa mutumin nan yake wadata ki da komai na rayuwa amma bai son maganar aure a tsakaninku?”
Bayan ya yi shiru na kamar daƙiƙa uku, sai ya ƙara cewa: “Auta, ki ƙara tambayar kanki; shin anya da gaske wannan mutumin yana son ki?”
_______________
Tsakure daga BABI NA UKU, a littafin KYALLIN NAIRA na Bashir Yahuza Malumfashi.













