SANA’AR NOMA: Ya Dace Attajirai Su Tallafa Wa Matasan Arewa – Dokta Sharif Almuhajir
~~~~~~~
A yayin da daminar bana ta fara nisa, Mujallar Taskar Gizago ta tuntuɓi Dokta Sharif Almuhajir, manomi a Jihar Yobe, domin jin hali da yanayin da damina take a yankin nasu. Haka kuma a matsayinsa na matashi, malamin jami’a, masanin tattalin arziki, za mu ji shawarwari daga gare shi, da zai ba matasan Arewa, dangane da noma da kiwo.
~~~~~~~


TG: Ko za mu fara da gabatar da kanka a taƙaice?
ALMUHAJIR: Farko dai sunana Sheriff Muhammad Ibrahim, wanda aka fi sani da Dokta Sheriff Almuhajir. Ni Associate Professor (Ɗangaladiman Farfesa) ne a bangaren Ilimin Tattalin Arzikin Addinin Musulumci (Islamic Financial Administration). Ina karantarwa a Jami’ar Jihar Yobe, sannan kuma a yanzu haka ni ne Shugaban Bankin Tallafa wa Ƙananan Masana’antu na Jihar Yobe (Yobe State Microfinance Bank).
Na yi karatun Alƙur’ani mai girma a matakin farko a makarantar Alƙur’ani da mahaifina ya assasa a garin Maiduguri. Sannan na je School for Higher Islamic Studies. Na yi sakandare, na yi digiri na farko a Jami’ar Maiduguri, na biyu a Jami’ar Usman Ɗanfodiyo da ke Sakkwato. Na yi wani digirin na biyu a Jami’ar Almadina International University. Sannan na yi digirin-digirgir (PhD) a University of Islamic Sciences da ke Malaysia. Kuma na kai shekaru goma sha biyar ina karantarwa a Jami’ar Jihar Yobe da ke Damaturu ya zuwa yanzu.
TG: Tun yaushe ka fara noma kuma yaya yanayin abubuwan da ka noma a bana, ko akwai alamar haske?
ALMUHAJIR: Da farko na fara noma ne ta ɓangaren kiwon dabbobi, musamman kajin Turawa tun ina ɗalibin a Jami’ar Maiduguri a shekarar 2001. Sannan na buɗe gona mai girma da nake sarrafawa a shekarar 2013. Daga bisani na bari na koma karatu a Malaysia, inda bayan na dawo na ci gaba da harkar noma tun a shekarar 2016 kuma har zuwa yanzun nan ban daina ba.
Sai dai bayan da aka naɗa ni Shugaban Yobe Microfinance Bank na fara muamala da ƙananan manoma, waɗanda muke bai wa ƙananan jari su yi noma, sannan su biya daga baya. Dayake muna bibiyar manoman domin tabbatar da cewa sun yi amfani da kuɗaɗen da muka ba su daidai, a hankali har na fara tunanin cewa lallai sana’ar noman abinci da sauran tsirrai tana da matuƙar muhimmanci ga rayuwar talaka, musamman ma ma’aikacin gwamnati. Saboda harkar noma za ta ba shi lokaci isassshe da zai yi aikinsa na gwamnati kuma ya kula da gonar tasa. Dalilin haka sai na fara shiga noman sosai.
Daga farko na fara ne da noman damuna. Na shuka gero a shekarar 2020, duk da ban tsaya na ba da kulawa irin yadda ya dace sosai ba, an samu albarka daidai gwargwado. A hankali har na dawo noman rani. A shekarar farko na noma alkama, daga baya na koma noma abubuwa da dama kamar shinkafa, masara, gero, gyaɗa, gangala, zoɓo, attarugu, tattasai da barkono. Kuma na shuka irin dabino guda dubu ashirin, sannan ina da burin zuwa gaba in ƙara shuka wasu abubuwan.
TG: Waɗanne irin ƙalubale kai kanka da manoman Jihar Yobe suke fuskanta, musamman a daminar bana?
ALMUHAJIR: Ƙalubale yana nan a harkar noma kamar yadda yake a kowacce harka amma ma fi girman ƙalubalen na manoma a Jihar Yobe ya ƙunshi jarin sana’ar noma, ƙarancin ruwan sama da na ƙasa a wasu wurare, ko’inkula na ma’aikatan gona, ambaliyar ruwa a wasu wurare, rashin ma’ajiyar kayan gona ingatacce da yake jawo lalacewar kayan gona, tsadar kayan aiki da kuɗin ma’aikata da kuma karyewar farashin kayan gona, musamman lokacin rani.
TG: A matsayinka na matashi, manomi, masanin tattalin arziki kuma malamin jami’a, ko za ka ba matasan Arewa shawarwari dangane da noma da kiwo domin jawo hankali da ƙarfafa gwiwa?
ALMUHAJIR: Shawara ta ga matasa ita ce, kowa yayi ƙoƙari ya rungumi aikin noma ko a matsayin sana’a ko a matsayin noman abinci, domin noma shi ne zai hutar da mu daga kukan hauhawar kayan abinci. Noma sana’a ce da kan iya riƙe mutum tsawon rayuwarsa, ba tare da ya nemi aiki a wajen wasu ba. Wanda ba shi da kuɗin mallakar gona sai ya nemi ta haya. Wanda ba shi da jarin noma ya je ya yi ƙwadago, a hakan zai koya kuma zai samu kuɗin noma tasa gonar nan gaba.
A ƙarshe, ina so in yi kira ga attajiranmu na yankin Arewa da su dawo da hankalinsu wajen ƙarfafa gwiwar matasa a kan abin da ya shafi harkar noma, saboda babu shakka wannan hanya ce da za ta samar da ayyukan yi, kuma ta sake bunƙasa tattalin arzikinsu da na ƙasa baki ɗaya.
~~~~~~~~













