Abin Da Ya Sa Muka Karrama Jami’an Tsaro A Malumfashi
– Injiniya Muntari Sagir
Daga Wakilinmu

_______________
Shugaban Kamfanin Gine-Gine na Muntasarab Global Concept Limited, Injiniya Muntari Sagir Malumfashi ya bayyana cewa babban abin da ya sanya suka karrama DPO na Malumfashi CSP Bello Umar da sauran jajirtattun jami’an tsaro da kuma dakarun tsaro na sa-kai da ke Ƙaramar Hukumar Malumfashi shi ne domin a jinjina masu kuma a ƙarfafa masu gwiwa, domin su ci gaba da yi wa al’umma hidima.
Injiniya ya bayyana haka ne a wata tattaunawa da wakilinmu, jim kaɗan kafin gudanar da walima ta musamman da kamfaninsa tare da haɗin gwiwar Masarautar Gadiman Katsina suka shirya.
“Kamar yadda ka sani, a kwanakin baya mai girma Gwamna, Malam Dikko Umar Radda ya karrama shi DPO na Malumfashi, saboda yabawa da ƙoƙarinsa a wannan gari namu, wajen tabbatar da tsaro. Don haka ne mu ma muka ga ya dace mu taya Gwamna wannan aiki, kasancewar garinmu ne kuma yankinmu ne ake wa wannan hidima.” In ji Muntari Sagir.
Baya ga DPO Bello Umar, wanda aka yi wa karramamawa ta musamman , an kuma karrama babban jami’in soja, Manjo Ajibade da kuma shugaban dakarun tsaron sakai na Malumfashi, Baba Sanusi. Haka kuma an karrama wasu zaɓaɓɓun mutane da dama, waɗanda suke ba da gudunmowa ta fuskar tsaro a Ƙaramar Hukumar Malumfashi.

A jawabinsa a zauren taron, Injiniya Muntari Sagir ya jinjina wa dukkan jami’an tsaro na gwamnati da ma ‘yan sa-kai, waɗanda ke taimakawa a kowane lokaci domin tabbatar da tsaro a yankin na Malumfashi. Ya buƙaci al’umma, musamman attajirai a yankin da su taimaka wa mabuƙata. “Babu shakka, a wannan lokaci al’umma na buƙatar taimako. Dom haka masu abin hannu su taimaka. Kuma ya kamata mu sani, ka ba da taimako ba ya sa abinka ya ƙare, sai ma albarka Allah zai sanya wa dukiyar taka.” In ji shi.
Bikin wanda ya gudana a zauren taro na tsohuwar Sakatariyar Ƙaramar Hukumar Malumfashi a yau Lahadi, ya samu halartar Shugaban Ƙaramar Hukumar Malumfashi, Alhaji Muntari Abdullahi da Galadiman Katsina, Jastis Sadiƙ Abdullahi Mahuta da Manajan Darakta na Hukumar Ruwa ta Jihar Katsina, Injiniya Tukur Hassan Tingilin da sauran manyan baƙi da dama.
_______________













