TAURARON GIZAGO: Idris Ibrahim Kubau
Gabatarwa:
A wannan karon, Malam Idris Ibrahim Kubau ne ya samu ɗarewa a kujerar TAURARIN GIZAGO. Mutum ne jajirtacce, saraki, mai sharhi kan al’amuran yau da kullum. Yana ɗaya daga cikin jigajigan da suke yin hidimar zumunci a wannan ƙungiya ta Gizago. Yana da himma ƙwarai, domin hasali ma, yana daga cikin ƙalilan ɗin mutanen da suka zama silar assasawa da kafa wannan ƙungiya.
Wane Ne Idris Ibrahim Kubau?
An haifi Idris Ibrahim Kubau a garin Kubau da ke Ƙaramar Hukumar Kubau cikin Jihar Kaduna. Ya yi karatun addini da na zamani har zuwa matakin digiri na biyu da kuma difloma a harkar ƙwarewa kan malanta, watau Professional Diplama in Education. Ya yi koyarwa a makarantar firamare ta gwamnati da sakandare, haka ma da makarantar Islamiyya na tsawon shekaru; don taimaka wa al`umma.
Yanzu haka yana aikin gwamnati da kuma noma. Yana da aure da yara. Haka kuma shi Basarake ne, domin kuwa shi ne Barden Kubau.
Manufarsa Game Da Gizago:
Manufarsa game da Ƙungiyar Gizago ta Najeriya ta taso ne saboda sha`awarsa kan rubuce-rubuce. Yana cikin ƙungiyoyi da dama, musamman Ƙungiyar Gizago, wadda yake matukar ƙauna don sada zumunci da ci gaban al`adun Hausa.
Matsayinsa A Ƙungiyar Gizago:
Malam Idris shi ne Shugaban Ƙungiyar Gizago na farko a Jihar Kaduna kuma shi ne Mataimakin Sakatare na farko na kasa. Lambarsa ta Gizago ita ce: GZG-64-KDN.
Ya ce: “Ina jinjina wa Malam Bashir Yahuza Malumfashi bisa wannan tunani na kafa wannnan ƙungiya da Alhaji Muntaƙa Abdulhadi Dabo, shugabanta na farko na ƙasa, bisa ganin ƙungiyar ta kafu da ƙokarin yin taro; muka san junanmu bayan haɗuwa a jarida da buga waya. Allah Ya saka musu da alheri.”
Fahimtarsa Game Da Zumunci:
Malam Idris Ibrahim Kubau ya ce: “Haƙiƙa zumunci abu ne mai matuƙar muhimmamci da kuma lada ga masu sadar da shi. Ƙungiyar Gizago ita ce ƙungiyar da na fi ƙauna da alfahari da ita saboda irin mutanen da ta haɗa, muka zama ‘yan uwa.”
Shawararsa Ga Gizagawa:
Ya ce: “Shawarwarina ga Gizagawa, su zama haƙuri da juna. Su zama masu jajircewa da dogaro da kai da taimakon juna. Su zama masu sada zumunci da riƙo da al`adunmu masu kyau.”














Ina godiya sosai Malam Bashir Yahuza Malumfashi kan wannan ƙoƙari naka. Allah Ya saka da alkhairi Ya bada lada Ya ƙara daukaka da yauƙaƙa danƙon Zumunci amin.