Musulmin Kudancin Najeriya Sun Jaddada Mubaya’a Ga Sarkin Musulmi
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Babban Limamin Jihar Oyo, Sheikh (Barrista) Bilal Husayn Akinola Akeugberu, ya sake jaddada aniyar ɗaukacin Musulmin yankin na bin jagorancin Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar, a dukkan lamurran da suka shafi addinin Musulunci.
Sheikh Akeugberu ya bayyana haka ne yayin da Musulmin yankin Yarabawa suka ci gaba da tsayin daka duk da yunƙurin wasu da suka kira masu haddasa rarrabuwar kai, waɗanda ke ƙoƙarin tunzura su su yi tawaye ga jagorancin al’ummar Musulmi ta Najeriya saboda dalilai na siyasa.
Ya ƙara da cewa wannan matsaya ta yi daidai da koyarwar Musulunci, yana mai jaddada cewa ta dace da Sunnah kamar yadda take a cikin Alƙur’ani Mai Girma da Hadisan Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi).
Tun da farko, Babban Limamin, wanda kuma lauya ne kuma tsohon Sakatare Janar na Ƙungiyar Kare Haƙƙin Musulmi (AMURIC), ya fitar da sanarwa daga ofishinsa cewa ba za a ayyana fara azumin watan Ramadan a Jihar Oyo kai tsaye ba tare da bin tsarin bai ɗaya da sauran Musulmin Najeriya ba.
A cikin sanarwar da ya sanya wa hannu da kansa, Sheikh Akeugberu ya ce Musulmin yankin Oyo za su jira sanarwar hukuma ta ganin jinjirin wata daga Sarkin Musulmi da ke Sakkwato, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, kafin fara azumin Ramadan.













