• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Saturday, April 18, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
February 13, 2026
in Labarai
0
Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

Sheikh Mutawakkil Mustapha yana hausawa da Gwamna Dikko Raɗɗa

34
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Bura women Celebrate Bukar Usman at 83

Ƙungiyar Matan Al’ummar Bura Sun Karrama Dr. Bukar Usman Bisa Cika Shekaru 83

January 9, 2026
Sheikh Mutawakkil Mustapha yana hausawa da Gwamna Dikko Raɗɗa

 

__________

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya rantsar da Sheikh Mutawakkil Mustapha Salis a matsayin Mai Girma Alƙalin Shari’a (Khadi) na Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Shari’a ta Jihar Katsina, tare da jan hankalinsa da ya riƙa aiki da gaskiya, adalci, da tsoron Allah wajen gudanar da aikinsa.

Bikin rantsuwar, wanda aka gudanar a jiya Asabar a Gidan Gwamnatin Jihar Katsina, ya samu halartar manyan baƙi daga ɓangarorin zartarwa, majalisa da shari’a na gwamnatin ta jiha, sarakunan gargajiya, malaman addinin Musulunci da ‘yan uwa da abokan arziki.

A wata takardar manema labarai, wacce Ibrahim Kaula Mohammed, Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnan Jihar Katsina ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa Gwamna Radda ya bayyana naɗin a matsayin wani mataki na ƙarfafa tsarin shari’ar Musulunci da inganta isar da adalci a faɗin jihar.

“Yau muna rantsar da sabon Mai Girma Alƙalin Shari’a na Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Shari’a ta Jihar Katsina. Wannan naɗi yana ƙarfafa tsarin shari’armu tare da inganta isar da adalci ga al’ummarmu,” in ji Gwamnan.

Ya taya sabon Alƙalin murna tare da yaba wa Hukumar Ayyukan Shari’a ta Jiha, kan gudanar da cikakken tsari na zaɓe bisa cancanta.

“Ofishinka babban nauyi ne. Dole ne ka riƙa tuna rantsuwar da ka yi kuma ta zama jagora ga ayyukanka. Dole ne a yi adalci ba tare da tsoro ko son rai ba,” in ji shi.

Gwamna Radda ya tunatar da sabon Alƙalin cewa mukaminsa amana ce mai girma a gaban Allah da al’umma. Yana mai kira gare shi da ya kasance mai bin adalci, gaskiya da koyarwar Musulunci.

“Bangaren shari’a shi ne mafaka ta ƙarshe ga talaka. Amincewar jama’a tana dogara ne kan gaskiya da ƙwazon ma’aikatan shari’a,” a cewar Gwamna.

Gwamnan ya kuma sake jaddada aniyar gwamnatinsa ta ci gaba da tallafa wa ɓangaren shari’a tare da inganta haɗin gwiwa tsakanin ɓangarori uku na gwamnati, domin tabbatar da zaman lafiya, tsari da adalci a jihar.

Daga cikin waɗanda suka halarta akwai Sakataren Gwamnatin Jiha, Abdullahi Garba Faskari; Kwamishinar Shari’a kuma Babbar Lauyan Jiha, Barrista Fadila Muhammad Dikko; da Babban Alƙalin Shari’a na Jihar Katsina, tare da sauran manyan baƙi.

Previous Post

Musulmin Kudancin Najeriya Sun Jaddada Mubaya’a Ga Sarkin Musulmi

Next Post

TSAKANIN ALI JITA DA SOJABOY: WANE NE YA FI GASKIYA?

Related Posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Labarai

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Bura women Celebrate Bukar Usman at 83
Labarai

Ƙungiyar Matan Al’ummar Bura Sun Karrama Dr. Bukar Usman Bisa Cika Shekaru 83

January 9, 2026
Sojoji Sun Ƙwato Muggan Makamai A Jihar Taraba
Labarai

Sojoji Sun Ƙwato Muggan Makamai A Jihar Taraba

January 5, 2026
Next Post
TSAKANIN ALI JITA DA SOJABOY: WANE NE YA FI GASKIYA?

TSAKANIN ALI JITA DA SOJABOY: WANE NE YA FI GASKIYA?

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

An Kama Wasu Mata Da Ke Safarar Makamai Zuwa Katsina

An Kama Wasu Mata Da Ke Safarar Makamai Zuwa Katsina

October 2, 2023
Nigerian Politicians: Leaders or Looters?

Nigerian Politicians: Leaders or Looters?

June 8, 2024
Gwamnati Ta Nemi Google Ya Daƙile Bazuwar Bayanan Da Ka Iya Wargaza Najeriya

Gwamnati Ta Nemi Google Ya Daƙile Bazuwar Bayanan Da Ka Iya Wargaza Najeriya

October 14, 2023
Matsalolin Tsaro: Ƙungiyar ‘Yan Jarida Ta Arewa Ta Shirya Taron Neman Mafita

Matsalolin Tsaro: Ƙungiyar ‘Yan Jarida Ta Arewa Ta Shirya Taron Neman Mafita

November 7, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Ko Me Ya Sa Manyan Mata Ke Auren Yara?
  • Mu Ji Tsoron Allah
  • Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Ko Me Ya Sa Manyan Mata Ke Auren Yara?

Ko Me Ya Sa Manyan Mata Ke Auren Yara?

April 18, 2026
Mu Ji Tsoron Allah

Mu Ji Tsoron Allah

April 17, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.