• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, August 14, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawa Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (4)

TSOKACI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
January 2, 2026
in Gizago
0
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawa Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (4)

Bashir Yahuza Malumfashi, yayin da yake gabatar da ƙasida a Bikin Ranar Marubutan Hausa Ta Duniya, da ya gudana a Jigawa, shekaranjiya

36
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawa Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (4)

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Tsakanin Maza Da Mata Wa Ya Fi Yawa A Duniya?

Tsakanin Maza Da Mata Wa Ya Fi Yawa A Duniya?

August 13, 2026

Tsakanin Rarara Da Pantami: Yayin Da Maroƙi Ya Zaci Shi Wani Ƙusa Ne…

August 2, 2026
Bashir Yahuza Malumfashi, yayin da yake gabatar da ƙasida a Bikin Ranar Marubutan Hausa Ta Duniya, da ya gudana a Jigawa, shekaranjiya

 

                      __________
√ Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Batun Ramuwar Gayya:
Ya ku ‘yan uwa masu bibiyar wannan muƙala da jimiri, a wannan fitowa kashi na huɗu, za mu ci gaba da bayani dangane da wasu munanan manufofi da muka ankara da su daga ‘ya’yan Ƙungiyar Hausawa Bogi, musamman yadda suke nuna su a kafafen sadarwa na zamani (Soshalmidiya).

Ga duk mai tu’ammali da waɗannan kafafe, babu shakka zai riƙa gamuwa da munanan kalaman masu ƙumajin kafa Ƙungiyar Hausawa Zalla. Ɗaya daga cikinsu shi ne, za su kafa wannan ƙungiya ce, kacokan da nufin haddasa gaba da ƙiyayya tsakanin al’ummar Arewa, musamman ma dai tsakanin Fulani da Hausawa. Babbar manufarsu ita ce, ramuwar gayya da ɗaukar fansa a kan musamman Fulani.

A ƙoƙarinsu na bayyana wannan muguwar manufa, ƙarara za ka ji sun kama sunan Mujaddadi Usman Ɗanfodiyo, suna zagin shi da tozarta shi; sannan kuma suna ƙirƙirar tarihin ƙarya suna jingina masa. Ba shi kaɗai ba, masu wannan ƙungiya ta Hausawa zalla, za ka ga suna ta haƙilon haddasa gaba da husuma tsakanin al’ummar Musulmi. Su a nufinsu, al’ummar Fulani gaba ɗayansu ‘yan ta’adda ne, don haka ya kamata Hausawa su tashi su yaƙe su gaba ɗaya.

To, abin tambaya a nan shi ne, shin anya kuwa akwai alheri ga ƙungiyar da take bijiro da irin waɗannan baƙaƙen halaye? Shin da gaske ne, cewa Sheikh Usman Ɗanfodiyo (ra) bai shuka alheri ba a ƙasar Hausa? Shin wai ma da suke kiran dukkan Fulani da sunan ‘yan ta’adda, musamman kasancewar wasu daga cikinsu suna garkuwa da mutane da ta’addanci a yankin nan, shin a rigar ƙungiyoyin Fulani suke gudanar da wannan ta’addanci? Shin wannan ta’addanci da wasu baragurbin Fulani suke aikatawa, Hausawa kaɗai suke kamawa da kashewa?

Za mu bi tambayoyin nan ɗaya bayan ɗaya, inda da yardar Allah, za mu ida fahimtar gaskiyar manufar masu ƙungiyar Hausawa, cewa ba wani abu suke ɗauke da shi ba sai babbar guba da dasisar wargaza al’ummar da ke zaune lafiya da juna na tsawon zamani.

Game da Sheikh Usman Ɗanfodiyo (ra) kuwa, babu shakka, duk wani mai kyakkyawan tunani, musamman idan dai shi Musulmi ne na ƙwarai; to ba zai taɓa kushe Mujaddadi ba. Domin kuwa Sheikh ya kafa babban tarihi, abin yabawa a duniyar Musulunci. Daular Muslunci ta Sakkwato da ya kafa, tun kimanin sama da shekara 200 da ta gabata, ta kasance daula mafi girma da bunƙasa a Afrika ta Yamma.

Ya jaddada Musulunci. Ya yaɗa ilimi. Ya kafa gwamnati mai tsari, abin alfaharin baƙar fata, tun kafin zuwan Turawa. Ya kafa tsarin tafiyar da al’umma mai cike da adalci da ɗa’a da nagarta – wanda har zuwa yau ana cin gajiyarsa.

Jama’a, yau ma a nan zan dakata. Sai kuma karo na gaba, in sha Allahu. A ci gaba da bibiyar mu da haƙuri. Muna kuma maraba da dukkan martani, ƙarin bayani ko tambaya a Comment Section.
_______________

Previous Post

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawa Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (3)

Next Post

Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci

Related Posts

Tsakanin Maza Da Mata Wa Ya Fi Yawa A Duniya?
Gizago

Tsakanin Maza Da Mata Wa Ya Fi Yawa A Duniya?

August 13, 2026

Tsakanin Rarara Da Pantami: Yayin Da Maroƙi Ya Zaci Shi Wani Ƙusa Ne…

August 2, 2026
Ko Yaya Za A Fassara Wannan Kallon?
Gizago

Ko Yaya Za A Fassara Wannan Kallon?

July 30, 2026
Next Post
Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci

Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Ta’aziyyar Ɗanbarno: Daga Fasihin Mai Zane Kamal Iyantama

Ta’aziyyar Ɗanbarno: Daga Fasihin Mai Zane Kamal Iyantama

July 5, 2023
JIDALIN KISHIYA – Labarin Uwargida Farida

JIDALIN KISHIYA – Labarin Uwargida Farida

September 3, 2024
Al’amuran Tsaro: Musulmin Duniya Sun Taru A Abuja

Al’amuran Tsaro: Musulmin Duniya Sun Taru A Abuja

August 12, 2026
58: ALHAMDU LILLAH

58: ALHAMDU LILLAH

May 14, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Our Daily Message
  • Regulation, Standardisation of Qur’anic Schools Under Way in Katsina
  • Gwamnati Za Ta Samar Da Ingantaccen Tsarin Gudanar Da Makarantun Alƙu’rani A Jihar Katsina

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Our Daily Message

Our Daily Message

August 14, 2026
Regulation, Standardisation of Qur’anic Schools Under Way in Katsina

Regulation, Standardisation of Qur’anic Schools Under Way in Katsina

August 13, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.