Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Fitaccen mawaƙi kuma marubucin waƙoƙi a Kudancin Najeriya, Kizz Daniel, ya jefar da addinin Kiristanci, ya rungumi Musulunci, kamar yadda jaridar intanet ta Nairaland ta ruwaito.
Kizz Daniel shi ne fitaccen mawaƙi na baya-bayan nan da ya amshi Musulunci, tun bayan wasu watannin baya da Burna Boy, ya canja daga Kirista zuwa Musulmi.
Kizz Daniel, wanda asalin sunansa Oluwatobiloba Daniel Anidugbe, ya taso ne yana bin addinin Kiristanci, duk da cewa an haife shi a cikin iyalin Musulmi. Sunansa na Musulunci shi ne Dhikrullah. Kizz Daniel yana da ƙani mai kama da shi sosai, mai suna Uthman Anidugbe, wanda ke aiki tare da shi.
Domin nuna tabbacin cewa shi cikakken Musulmi ne a yanzu, an jiyo mawaƙi Kizz Daniel a wani faifan bidiyo da ya bazu a kafafen sada zumunta, inda wani ɗan Masar da wani ɗan Iraƙi suke kiran Sallah da murya mai daɗi; in da ya nuna sha’awarsa ga sautin muryoyin matasan Larabawan biyu. Bayan da suka gama kiran Sallar, sai shi Daniel ya ce: “Ma sha Allah.”
__________













