• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Monday, July 27, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

Gobara Daga Kogi: Malamin Islamiyya Ya Lalata Ɗalibansa 9 Da Luwaɗi

BABBAN LABARI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
December 14, 2025
in Babban Labari
0
Gobara Daga Kogi: Malamin Islamiyya Ya Lalata Ɗalibansa 9 Da Luwaɗi

Allah ka kiyashe mu da mugun ji da mugun gani!

57
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Gobara Daga Kogi: Malamin Islamiyya Ya Lalata Ɗalibansa 9 Da Luwaɗi

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Budurwa Mai Aikin Tausa Ta Mutu A Gidan Minista

Budurwa Mai Aikin Tausa Ta Mutu A Gidan Minista

July 15, 2026
Jami’an Tsaro Sun Ceto Ɗalibai da Malaman Oyo

Jami’an Tsaro Sun Ceto Ɗalibai da Malaman Oyo

July 11, 2026
Sanarwar: Wannan hoto samfoto ne aka ƙirƙira da Fasahar AI. Allah ka kiyashe mu da mugun ji da mugun gani!


                              •••••••
Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un!
A makon da ya gabata ne aka samu wani mummunan lamari da ya faru a Abuja, inda aka samu wani malamin Islamiyya da tuhumar lalata ɗalibansa guda tara da luwaɗi.

Lamarin, wanda za mu danganta shi da gobara daga kogi, maganinta Allah, Ordinary President, Dokta Ahmad Isah tare da ma’aikatansa ne suka gudanar da bincikensu, a sashen Hausa na gidan rediyon Human Rights Radio, Abuja.

A shirin, an gabatar da yaran su 9, waɗanga suka kasance ‘yan shekara 10, 11 zuwa 12 kuma kowannensu ya yi bayani dalla-dalla, ya fayyace yadda malamin ya riƙa yaudara da tsorata su, ya riƙa kai su gidansa yana wannan aika-aika, har zuwa wannan lokaci da asirinsa ya tonu.

Babu shakka wannan lamari ya yi muni matuƙa, domin kuwa wasu daga cikin yaran, ana zargin sun kamu da cuta, domin suna wahala wajen zama da mazaunansu. Akwai ƙunci da ciwo ga iyayen yara, su tura ‘ya’yansu wurin da suke zaton aminci da tarbiyya da addini, amma wurin ya rikiɗe zuwa inda za a lalata masu rayuwa!

A Musulunci, luwaɗi babban zunubi ne mai muni, wanda ya saɓa wa halittar da Allah ya yi wa ɗan Adam. Wannan abu da mutumin nan ya aikata ga waɗannan ƙananan yara, laifi ne, zalunci ne kuma cin amana ne da ba za a taɓa yarda da shi ba. Wannan mummunar ɗabi’a tana lalata tarbiyya, tana ɓata rayuwar yara, tana kuma iya ɓarar da rayuwar al’umma gaba ɗaya.

Alƙur’ani ya yi bayani a fili game da munin wannan aiki. A cikin Suratul A’araf, aya ta 81, Allah Maɗaukakin Sarki ya ce game da mutanen Annabi Luɗ (AS): “Kun zo wa maza domin sha’awa maimakon mata. A’a, ku mutane ne masu wuce gona da iri.”

Haka kuma Manzon Allah (SAW), a hadisin Tirmizi da Ibn Majah ya ce: “Ku kashe mai aikata luwaɗi da wanda aka yi wa.” Wannan ya nuna irin girman zunubin, domin babu wani laifi da aka yi bayani da tsanani irin haka face kaɗan.

Game da illolin da ke tattare da luwaɗi ga al’umma kuwa, laifi irin wannan ba wai kawai yana ɓata tarbiyya da mutunci ba ne, yana kuma iya haddasa cututtuka, lalata ƙwaƙwalwa da tsarin tunani. Yana kuma jawo tsanar iyaye da rashin kwanciyar hankali a cikin gida. Yaran da aka zalunta da wannan mummunan aiki, sukan girma cikin tsoro, damuwa ko rikicewar ɗabi’a. Munin wannan aiki babba ne kuma abin tsana ne ga al’umma musulma. Ya zama dole mu tsare amanar `ya’yanmu da mutuncinsu.

Musulunci ya umurci jama’a su riƙa hana juna masha’a, su zama masu tsare ‘ya’ya, tsarkake muhalli da kula da ƙananan yara. A wani hadisi da Bukhari da Muslim suka ruwaito, Manzon Allah (SAW) ya ce: “Dukkanku makiyaya ne kuma kowane mutum za a tambaye shi kan abin da yake kiyayewa.” Wajibi ne a wayar da kai cikin makarantu, masallatai da gidaje domin ceton ‘ya’ya daga hannun masu mugun nufi irin wannan malami na Islamiyya.

Ya zama wajibi ga hukumomi watau ‘yan sanda, kotuna, lauyoyi da ma’aikatar jin ƙai da kariyar yara, su tabbatar da cewa an hukunta mutumin da ya aikata wannan mummunan laifi. Hakan zai zama izina kuma domin kare al’umma, koya darasi da tabbatar da cewa irin wannan ƙazamar ɗabi’a ba ta sake samun gindin zama a cikin al’ummar Musulmi ba.

Ya Allah ka kare ‘ya’yanmu, ka tsare al’ummarmu daga fitina. Ka kuma shiryar da masu aikata irin waɗannan munanan ayyuka zuwa turba ta gaskiya. Amin.
_______________

Previous Post

Dokta T.S SAULAWA: Hadimin Al’umma A Koyaushe

Next Post

Philip Chikwuedo Asiodu: A Legacy of Dedication and Service

Related Posts

Budurwa Mai Aikin Tausa Ta Mutu A Gidan Minista
Babban Labari

Budurwa Mai Aikin Tausa Ta Mutu A Gidan Minista

July 15, 2026
Jami’an Tsaro Sun Ceto Ɗalibai da Malaman Oyo
Babban Labari

Jami’an Tsaro Sun Ceto Ɗalibai da Malaman Oyo

July 11, 2026
ACF Endowment Fund Sets Agenda for Transparency, Education and Empowerment in Northern Nigeria
Babban Labari

Asusun Tallafi na ACF Ya Tsara Sabuwar Hanyar Bunƙasa Ilimi da Ƙarfafa Al’ummar Arewa

June 25, 2026
Next Post
Philip Chikwuedo Asiodu: A Legacy of Dedication and Service

Philip Chikwuedo Asiodu: A Legacy of Dedication and Service

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Ya Kamata Marubuta Mu Karkata Alƙalaminmu Ga Matsalolin Al’umma

Ya Kamata Marubuta Mu Karkata Alƙalaminmu Ga Matsalolin Al’umma

May 26, 2025
NAJERIYA: Wannan Ba Lokacin Shagala Ba Ne

NAJERIYA: Wannan Ba Lokacin Shagala Ba Ne

May 31, 2023
Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

April 11, 2026
BELLO GALADANCHI: Burina In Ƙwato Wa Talakawa ‘Yanci Daga Azzaluman Shugabanni

BELLO GALADANCHI: Burina In Ƙwato Wa Talakawa ‘Yanci Daga Azzaluman Shugabanni

October 23, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • General Buratai to Marry Off His Daughter Today
  • Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya
  • Saƙon Godiya Da Bangajiya

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

General Buratai to Marry Off His Daughter Today

General Buratai to Marry Off His Daughter Today

July 25, 2026
Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya

Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya

July 24, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.