Gobara Daga Kogi: Malamin Islamiyya Ya Lalata Ɗalibansa 9 Da Luwaɗi
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un!
A makon da ya gabata ne aka samu wani mummunan lamari da ya faru a Abuja, inda aka samu wani malamin Islamiyya da tuhumar lalata ɗalibansa guda tara da luwaɗi.
Lamarin, wanda za mu danganta shi da gobara daga kogi, maganinta Allah, Ordinary President, Dokta Ahmad Isah tare da ma’aikatansa ne suka gudanar da bincikensu, a sashen Hausa na gidan rediyon Human Rights Radio, Abuja.
A shirin, an gabatar da yaran su 9, waɗanga suka kasance ‘yan shekara 10, 11 zuwa 12 kuma kowannensu ya yi bayani dalla-dalla, ya fayyace yadda malamin ya riƙa yaudara da tsorata su, ya riƙa kai su gidansa yana wannan aika-aika, har zuwa wannan lokaci da asirinsa ya tonu.
Babu shakka wannan lamari ya yi muni matuƙa, domin kuwa wasu daga cikin yaran, ana zargin sun kamu da cuta, domin suna wahala wajen zama da mazaunansu. Akwai ƙunci da ciwo ga iyayen yara, su tura ‘ya’yansu wurin da suke zaton aminci da tarbiyya da addini, amma wurin ya rikiɗe zuwa inda za a lalata masu rayuwa!
A Musulunci, luwaɗi babban zunubi ne mai muni, wanda ya saɓa wa halittar da Allah ya yi wa ɗan Adam. Wannan abu da mutumin nan ya aikata ga waɗannan ƙananan yara, laifi ne, zalunci ne kuma cin amana ne da ba za a taɓa yarda da shi ba. Wannan mummunar ɗabi’a tana lalata tarbiyya, tana ɓata rayuwar yara, tana kuma iya ɓarar da rayuwar al’umma gaba ɗaya.
Alƙur’ani ya yi bayani a fili game da munin wannan aiki. A cikin Suratul A’araf, aya ta 81, Allah Maɗaukakin Sarki ya ce game da mutanen Annabi Luɗ (AS): “Kun zo wa maza domin sha’awa maimakon mata. A’a, ku mutane ne masu wuce gona da iri.”
Haka kuma Manzon Allah (SAW), a hadisin Tirmizi da Ibn Majah ya ce: “Ku kashe mai aikata luwaɗi da wanda aka yi wa.” Wannan ya nuna irin girman zunubin, domin babu wani laifi da aka yi bayani da tsanani irin haka face kaɗan.
Game da illolin da ke tattare da luwaɗi ga al’umma kuwa, laifi irin wannan ba wai kawai yana ɓata tarbiyya da mutunci ba ne, yana kuma iya haddasa cututtuka, lalata ƙwaƙwalwa da tsarin tunani. Yana kuma jawo tsanar iyaye da rashin kwanciyar hankali a cikin gida. Yaran da aka zalunta da wannan mummunan aiki, sukan girma cikin tsoro, damuwa ko rikicewar ɗabi’a. Munin wannan aiki babba ne kuma abin tsana ne ga al’umma musulma. Ya zama dole mu tsare amanar `ya’yanmu da mutuncinsu.
Musulunci ya umurci jama’a su riƙa hana juna masha’a, su zama masu tsare ‘ya’ya, tsarkake muhalli da kula da ƙananan yara. A wani hadisi da Bukhari da Muslim suka ruwaito, Manzon Allah (SAW) ya ce: “Dukkanku makiyaya ne kuma kowane mutum za a tambaye shi kan abin da yake kiyayewa.” Wajibi ne a wayar da kai cikin makarantu, masallatai da gidaje domin ceton ‘ya’ya daga hannun masu mugun nufi irin wannan malami na Islamiyya.
Ya zama wajibi ga hukumomi watau ‘yan sanda, kotuna, lauyoyi da ma’aikatar jin ƙai da kariyar yara, su tabbatar da cewa an hukunta mutumin da ya aikata wannan mummunan laifi. Hakan zai zama izina kuma domin kare al’umma, koya darasi da tabbatar da cewa irin wannan ƙazamar ɗabi’a ba ta sake samun gindin zama a cikin al’ummar Musulmi ba.
Ya Allah ka kare ‘ya’yanmu, ka tsare al’ummarmu daga fitina. Ka kuma shiryar da masu aikata irin waɗannan munanan ayyuka zuwa turba ta gaskiya. Amin.
_______________













