• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Monday, May 25, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Wasanni

Matsalolin Da Suka Daƙile Super Eagles Daga Gasar Kofin Duniya

WASANNI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
November 17, 2025
in Wasanni
0
Matsalolin Da Suka Daƙile Super Eagles Daga Gasar Kofin Duniya

'Yan wasan Super Eagles na Najeriya

36
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Matsalolin Da Suka Daƙile Super Eagles Daga Gasar Kofin Duniya

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
PSG DA ARSENAL: ZARATAN ‘YAN WASAN DA ZA SU BA DA MAMAKI

PSG DA ARSENAL: ZARATAN ‘YAN WASAN DA ZA SU BA DA MAMAKI

April 29, 2025
‘Yan wasan Super Eagles na Najeriya

 

                              •••••••
A jiya ne Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta ƙasar DR Congo ta doke Ƙungiyar Super Eagles ta Najeriya, a ƙoƙarinta na samun gurbin fafatawa a Gasar Kofin Duniya da za a gudanar a ƙasar Qatar a baɗi. Matsaloli da yawa sun taka rawa wajen daƙile himmar Super Eagles. Ga wasu daga ciki:

√ Yawan Sauya Ƙwararrun Masu Horar Da Super Eagles:
Ɗaya daga cikin manyan matsalolin da Najeriya ta sha wahala da su, ita ce rashin daidaiton horo. A yayin yaƙin neman gurbi a gasar ta baɗi, Super Eagles sun yi amfani da masu horarwa daban-daban, waɗanda suka haɗa da Peseiro, Finidi George da kuma Eric Sekou Chelle. Wannan rashin daidaito na masu horar da ƙungiyar, ya taka rawa wajen daƙile ƙungiyar daga samun tsarin wasa guda ko salon da aka dogara da shi, wanda ya shafi haɗin kan ‘yan wasa a yayin da suka shiga filin wasa.

√ Ƙarancin Himma da Rashin Mayar da Hankali a Wasanni Masu Matuƙar Muhimmanci:
A wasu lokuta, Super Eagles sun ja wa kansu rashin nasara ko kuma samun sakamako mara kyau a wasansu da ƙungiyoyi da ake ganin ba su da ƙarfi sosai. Misali, sun yi canjaras da ƙasashen Lesotho (1–1), Zimbabwe da kuma asara mai zafi a wasansu da ƙasar Benin, bayan kuma su suka fara da cin ƙwallo. Wannan ya nuna akwai matsalar rashin mayar da hankali a lokutan da ake tsammanin samun nasara cikin sauƙi.

√ Rashin Tsari Daga Gwamnati Da Hukumar Kwallon Ƙafa Ta Najeriya:
Akwai rahotanni cewa Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Najeriya (NFF) ba ta tafiyar da abubuwa yadda ya kamata ba. An ce akwai matsalolin kuɗi, rashin biyan albashi da bashi na horo ga ’yan wasa da ma’aikata da kuma rashin gaskiya da bin ƙa’idoji. Bugu da ƙari, wasu suka nuna cewa NFF ba ta sanya himma ba sosai wurin duba filayen wasa da yanayinsu. Wani rahoto ya ce filin wasa da Najeriyar za ta buga a ƙasar Afirka ta Kudu bai dace ba kuma NFF ba ta yi ƙoƙarin kawo gyara ba. Haka ma wajen zaɓen ‘yan wasa, akwai ƙorafin cewa ana sanya son kai, ƙabilanci da ɓangaranci ko karɓar cin hanci, kafin a saka ɗan wasa a Super Eagles. An nuna cewa, ana zaɓen ‘yan wasa mafi yawa daga Kudu, ana barin ƙwararru da suka fito daga Arewa.

Matsalolin Fasaha a Wasanni:
A ɓangaren wasanni, Super Eagles sun nuna rauni a wasu sassa, musamman wajen kare gidansu (defense) da kuma sarrafa wasan tsakiya. Rahotanni sun bayyana rashin haɗin kai a tsakanin ’yan tsaron ƙungiyar (centre-backs) da matsalolin maki a manyan lokuta. Haka kuma, ba su nuna ƙarfi sosai a wajen kai hari ga abokan hamayya ba; duk da cewa suna da ’yan wasa ƙwararru da ke buga ƙwallo a manyan ƙungiyoyin ƙasashen Turai. Wannan sakaci ya hana su samun maki wadatacce a wasu wasanni.

√ Rashin Nuna Kishin Ƙasa:
A cewar Moses Simon (ɗaya daga cikin manyan ’yan wasan Super Eagles), “akwai buƙatar kowa ya nuna kishi, ya yi abin da zai taimaka wa ƙungiyarsu domin samun nasara. Tun daga mai tsaro zuwa ɗan gaba, duk suna iya ba da gudunmawa.” Wannan magana na nuni da cewa akwai matsalar rarrabuwar kai da rashin kishi, inda wasu ’yan wasa suke iya yin ƙoƙari sosai, yayin da wasu ba su ba da cikakkiyar gudunmawa.

Gazawar Super Eagles wajen samun dama zuwa Gasar Kofin Duniya ta 2026, ba ta samo asali daga matsala guda ɗaya ba, sai daga haɗuwar matsalolin da suka haɗa da manyan matsalolin da muka zayyano a sama. Idan ƙungiyar za ta gyara waɗannan abubuwa, ta hanyar samar da ƙwararren mai horo mai ɗorewa, inganta aikin hukumar ƙwallon ƙafa, samar da tsari mai kyau a filin wasa da ƙarfafa haɗin kai a tsakanin ’yan wasa da kishin ƙasa. Haka kuma a daure a riƙa ɗauko ‘yan wasa daga dukkan sassan Najeriya, akwai yiwuwar su dawo cikin ƙarfinsu kuma su sake fafatawa a manyan gasanni nan gaba.
_______________

Previous Post

Haramta Koyarwa Da Harshen Uwa: Koma Baya Ko Cigaba?

Next Post

Janar M.B. Uba: Muzakkarin Da Ya Sadaukar Da Ransa Ga Najeriya

Related Posts

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco
Wasanni

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
PSG DA ARSENAL: ZARATAN ‘YAN WASAN DA ZA SU BA DA MAMAKI
Wasanni

PSG DA ARSENAL: ZARATAN ‘YAN WASAN DA ZA SU BA DA MAMAKI

April 29, 2025
UEFA 2025: WACE ƘUNGIYA CE ZA TA ƊAUKI KOFIN ZAKARU?
Wasanni

UEFA 2025: WACE ƘUNGIYA CE ZA TA ƊAUKI KOFIN ZAKARU?

April 28, 2025
Next Post
Janar M.B. Uba: Muzakkarin Da Ya Sadaukar Da Ransa Ga Najeriya

Janar M.B. Uba: Muzakkarin Da Ya Sadaukar Da Ransa Ga Najeriya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

HAWAYE DON AFIRKA

HAWAYE DON AFIRKA

August 16, 2023
Barkanmu Da Shiga Watan Dhul-Hijjah 1447

Barkanmu Da Shiga Watan Dhul-Hijjah 1447

May 18, 2026
AN DAKATAR DA MALAMIN MUSULUNCI DAGA YIN WA’AZI

AN DAKATAR DA MALAMIN MUSULUNCI DAGA YIN WA’AZI

November 19, 2024
ALI BABA: Tattaunawa Ta Musamman Da Marubucin Littattafan Musulunci

ALI BABA: Tattaunawa Ta Musamman Da Marubucin Littattafan Musulunci

July 29, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • POSITIVE COMRADE
  • BUKAR USMAN: The Human Library
  • Sule Lamido’s Theme of Authenticity

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

POSITIVE COMRADE

POSITIVE COMRADE

May 20, 2026
BUKAR USMAN: The Human Library

BUKAR USMAN: The Human Library

May 19, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.