AN DAKATAR DA MALAMIN MUSULUNCI DAGA YIN WA’AZI
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Hukumomi a Jihar Neja sun bayyana cewa za su miƙa wa Hukumomin jami’an tsaron Najeriya rahoto dangane da wani malami mai suna Muhammad bin Muhammad, wanda yake gabatar da wa’azin Musulunci ta hanyar da ba ta dace ba, hanyar da ka iya haddasa fitina tsakanin al’umma.
Shugaban Hukumar Kula da Al’amuran Addinai a Jihar ta Neja, Malam Umar Faruk ya bayyana wa manema labarai cewa hukumarsu ta dakatar da malamin daga ci gaba da wa’azi ne bayan binciken da suka gudanar a kansa.
A cewar sa, “kwamitin da muka kafa ya kira shi kuma mun tattauna da shi, mun gano cewa bai ma yi karatu ba.”
Shi dai Malam Muhammad, tun da farko an zarge shi da cewa ya daɗe yana gabatar da wa’azijin da kan kawo tashin fahimta a cikin al’umma. Kuma yana gudanar da ayyukansa a garin Tafa da ke Jihar Neja. Yana gudanar da makarantar Islamiyya kuma yana da mabiya wadanda ke halartar darussansa.
“Da muka lura cewa tafiyarsa da aƙidarsa da da’awarsa akwai hatsari ga tsaron Jihar Neja da ƙasa baki ɗaya, shi ne muka yanke hukuncin cewa a dakatar da shi kuma a rufe makarantarsa har sai jami’an tsaro sun yi bincike a kansa,” in ji Sheikh Faruk.
Ko a ‘yan kwanakin nan, ya gabatar da wa’azi, inda yake kafirta duk wanda yake ɗaukar hoto, kamar kuma yadda ya rika kama sunayen malaman Musulunci na Najeriya, yana cewa ‘yan wuta ne kuma mabiyansu ma ‘yan wuta ne.
Ya ƙara da cewa malamin yana kira ne ga magoya bayansa da su ƙaurace wa zaɓuka da duk wani abin da ya shafi dimokuraɗiyya.













