Galadiman Katsina Ya Karrama Ni Matuƙa
– Waziri Shehu Musa

__________
A jiya Asabar, 03-05-1447 (Hijiriyya), 25-10-2025 (Miladiyya), Galadiman Katsina, Hakimin Malumfashi, Mai Shari’a Sadiƙ Abdullahi Mahuta, OFR ya naɗa sabon Wazirin Galadiman Katsina, Alhaji Shehu Musa Ɗankano. Bashir Yahuza Malumfashi, Fasihin Galadiman Katsina-I ya tattauna da sabon Wazirin, a gidansa da ke Malumfashi; inda ya bayyana cewa wannan sarauta, karramawa ce gare shi daga Galadiman Katsina. Ga yadda tattaunawar ta kasance:
__________
TG: Ga shi a yau Allah ya tabbatar da naɗinka a sarautar Wazirin Galadiman Katsina, ko yaya kake ji a ranka a yau?
Waziri: Alhamdu lillah. Babu shakka zan fara da godiya ga Allah (swt) da wannan ni’ima da ya yi mani. Haka kuma ina godiya ga mai girma Galadiman Katsina, Mai Shari’a Sadiƙ Abdullahi Mahuta, OFR da wannan sarauta da ya ba ni ta Wazirin Galadiman Katsina. Babu shakka wannan sarauta, babbar karramawa ce a gare ni. Lallai kuma ina farin ciki matuƙa a yau. Allah saka da alheri.

TG: Yanzu ka tashi daga Ɗan Iyan Galadiman Katsina ke nan?
Waziri: Wannan gaskiya ne, daga yau na zama Wazirin Galadiman Katsina. Da ma a zamanin marigayi Galadiman Katsina na 10, Jastis Mamman Nasir ne Ya naɗa ni Sarautar Ɗan Iyan Galadiman Katsina. A yau wannan sarauta ta Ɗan Iya ta koma kan babban ɗan Galadima Sadiƙ Abdullahi Mahuta. Wannan sarauta ta Waziri, ita ce mafi girma daga Galadima. Wato daga shi Ubanƙasa Galadima, sai kuma ni Waziri.

TG: Ko kai ne na farko da aka taɓa ba wannan sarauta ta Waziri a Masarautar Galadiman Katsina?
Waziri: A’a, ba ni ne na farko ba. A can baya, an taɓa naɗa kawunmu, Bello Adamu a sarautar Wazirin Galadiman Katsina. Ya rasu kimanin watanni biyar da suka gabata. Ke nan, ni ne na biyu a wannan sarauta da aka naɗa a yau, bisa hukuncin Allah.

TG: Waɗanne irin ayyuka ne suka jiɓinci wannan sarauta ta Wazirin Galadiman Katsina?
Waziri: Muhimman ayyukan da suka hau kaina, a matsayina na Wazirin Galadiman Katsina sun haɗa da bayar da shawarwari ga shi mai girma Galadima, domin kyautata masarautar gaba ɗaya. Na biyu, tabbatar da cewa dukkan al’amuran da suka shafi masarautar Galadima suna tafiya daidai yadda suka kamata, ko Galadima na nan, ko ba ya nan. Wannan amana ce babba a kaina in kula da al’amuran masarautar. Haka kuma aikina ne in saurari al’ummar masarautar, in ji kokensu, Sannan in sanar da Galadima, a tattauna yadda za a magance su. Haƙƙin Galadima ne a sanar da shi abin da ke faruwa a masarautarsa – wannan aikina ne.

TG: Bisa la’akari da cewa an san ka da jajircewa wajen hidimar al’umma, a yanzu ga sabon nauyi ya ƙara hawa kanka. Shin me al’umma za su tsumaya daga gare ka?
Waziri: Alhamdu lillahi. A duk lokacin da mutum yake tafiyar da ayyukansa domin Allah, to haka lamarin ke kasancewa a gare shi. Ni dai ban yi tsammanin samun wannan babbar sarauta ba, sai ga shi Allah ya hukunta. Galadima ya yi la’akari da abubuwan da nake yi a baya da kuma abubuwan da zan iya yi a nan gaba in sha Allah, su ne suka sanya ya girmama ni da wannan sarauta. Sarauta ce mai ƙima kuma mai daraja sosai. Don haka da yardar Allah zan yi iya ƙoƙarina wajen ganin na ci gaba da yi wa al’umma hidima da kare martabar ita kanta sarautar da ma garinmu, jiharmu da ƙasarmu baki ɗaya.
TG: Malumfashi da kewaye na fuskantar matsalolin tsaro a wannan lokaci, a matsayinka na sabon Wazirin Galadima, wace shawara za ka ba jami’an tsaro da shugabanni, domin ganin an magance wannan ƙalubale na tsaro a wannan yanki?
Waziri: Babbar shawarar da zan ba da ita ce, a yi duk mai yiwuwa, a ƙokarta a kawo ƙarshen wannan matsala ta tsaro. Babu shakka mutane suka cikin matsala, domin ba su iya zuwa gona cikin aminci. Masu sana’o’i da kasuwanci suna fuskantar matsaloli. Shugabanni da jami’an tsaro suna ƙoƙari amma su ƙara himma, domin ganin Allah ya agaza mana, domin kawo ƙarshen matsalar.
Fulanin da ake zargi da wannan al’amari, ‘yan ƙasa ne ba bare ba, don haka a saurare su, a tsaya a yi gyara na kirki. Su ma ana jin suna kawo ƙorafe-ƙorafensu. A tara masana da masu ruwa da tsaki a zauna a tattauna lamarin nan, a yi wa kowa adalci, domin magance matsalar nan. Ta haka za a samu zaman lafiya da aminci.

TG: Ma sha Allah. Muna taya ka murna kuma Allah ya taya ka riƙo.
Waziri: To, Malam Bashir, Fasihin Galadima, ina godiya. Allah saka da alheri.
__________













