Ya Zama Wajibi A Tallafa Wa Matasa A Masarautar Galadiman Katsina
– In Ji Hasken Fadar Galadiman Katsina
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Hasken Fadar Galadiman Katsina, Alhaji Kabir Lawal 3030 ya yi kira da babbar murya ga attajirai da manyan ma’aikatan gwamnati na Masarautar Galadiman Katsina a Ƙaramar Hukumar Malumfashi, Jihar Katsina da su riƙa tallafa wa matasa yadda ya kamata, musamman wajen sama masu ayyukan yi, koya sana’o’i da kuma tallafin karatu, domin magance zaman kashe wando da gararamba a titi.
Alhaji Kabir 3030, wanda kuma shi ne Sarkin Hausawan Owerri, Jihar Delta, ya bayyana cewa rashin aikin yi ko sana’a da matasa suke yi, shi yake haddasa suke faɗawa cikin harkokin shaye-shaye da kuma shiga muggan ƙungiyoyin aikata manyan laifuka da sauransu. Ya jadadda cewa, babbar hanyar da za a magance matsalolin tsaro a yankunan Masarautar Galadima da ma Jihar Katsina baki ɗaya, shi ne gwamnati da masu hannu da shuni da manyan ma’aikatan gwamnati su riƙa jan matasa a jika, suna tallafa masu da aikin yi ko sana’a da kuma ɗaukar nauyin karatunsu.
Da yake ƙarin haske kan lamarin a wata tattaunawa ta musamman da wakilinmu, Hasken Fadar Galadima ya ba da misali da shi kansa, ya ce: “An haife ni a Unguwar Dawo, Ƙaramar Hukumar Malumfashi, Jihar Katsina. Na yi makarantar firamare a Tunau Primary School da kuma Unguwar Dawo Primary School, Malumfashi. Kuma tun da na taso, ban yi zaman banza ba, na ci gaba da neman ilimi,” in ji shi.
Ya ce ya ci gada da karatun sakandare a Government Day Secondary School Ɗanrimi, Malumfashi, inda ya yi aji uku, daga nan kuma ya ci gaba a Government College Katsina, inda yana aji biyu na babbar sakandare, ya sake canja makaranta.
A cewarsa, “Na ci gaba da karatun aji uku a babbar sakandare, a Arabic Teachers’ College Katsina, inda bayan na kammala, na shiga aikin ‘yan sanda kai tsaye.”
Da yake bayani game da sarautarsa ta Hasken Fadar Galadiman Katsina, Alhaji Kabir 3030 ya ce an naɗa shi wannan sarauta a ranar 12 ga watan Oktoba, shekara ta 2024.
“Mai girma Galadiman Katsina na 11, Mai Shari’a Saddiƙ Abdullahi Mahuta ne ya naɗa ni wannan sarauta ta Hasken Fada, bisa cancanta. Kaɗan daga cikin ayyukana a wannan masarauta, sun haɗa da bayar da muhimman shawarwari ga masasauta, domin bunƙasa al’umma, bayar da tallafi ga al’umma, musamman matasa ta hanyoyin da Allah ya hore mani da kuma kare martabar masarautar a ko’ina a faɗin duniya,” in ji 3030.
“A halin yanzu haka, ina tare da matasa ƙimanin 340, ina sama masu aiki da hanyoyin sana’a. A duk lokacin da dama ta samu, nakan yi amfani da ita wajen tallafa wa matasan Masarautar Galadiman Katsina.”
Alhaji Kabir 3030 ya ci gaba da cewa: “A nan Owerri, ni ne Sarkin Hausawa kuma ina samun damarmamaki da guraben aiki a kamfanoni. Nakan ɗauko matasanmu daga gida, in yi masu jagora su samu abin dogaro da kai.”
Hasken Galadima ya shawarci matasa da su guji zaman banza, su guji shaye-shaye. “A matsayinka na matashi, ka kama sana’a komai ƙankantarta, idan ka riƙe za ta bunƙasa. Ba sai ka jira aikin gwamnati ba. Ni a ra’ayina, na fi ba matasa shawara su kama sana’a, ba aikin gwamnati ba,” in ji shi.
Game da matsalar tsaro da take addabar masarautar Galadima da ma Jihar Katsina baki ɗaya, Alhaji Kabir 3030 ya ce ya kamata masarauta ta ba matasa muhimmanci, a tattara su, a riƙa ba su horo da kayan aiki, domin aikin tsaro na sa-kai. “Ni a misali, na ɗauki matasa sama da 30 a unguwarmu suna aikin tsaron unguwa. Na haɗa kansu, ina ba su shawararwari da kayan aiki, kamar tocila da sauransu, daidai gwargwadon abin da Allah ya hore mani.”
Wakilinmu ya tambayi Hasken Fada, shin ko Alhaji Kabir 3030 yana sha’awar shiga harkokin siyasa? Ya amsa da cewa:
“Ba ni da ra’ayin siyasa a rayuwata. Ko da na kammala aiki, kasuwanci zan kama. Ina da jama’a amma ba zan shiga siyasa ba saboda na san illarta. Ba na son in kasa sauke nauyin da Allah ya ɗora mani.”
Da yake yaba wa Galadiman Katsina kuwa, Hasken Fada Kabir 3020 ya ce: “Galadima Jastis Saddiƙ dattijo ne. A ra’ayina, ba a taɓa samun Galadima kamarsa ba a matsayin Hakimin Malumfashi. Bai da baƙin ciki, bai da girman kai, yana amsar kowa ba tare da wariya ba. Yana tafiyar da mulkinsa bisa daidai.”
Hasken Galadiman Katsina, Alhaji Kabir Lawal 3030 ya ƙarƙare da addu’a ga Galadima. “Tsakanina da Galadima sai fatan alheri. Allah ya sa ya gama mulkinsa lafiya kuma ya rabu da duniyar nan lafiya. Daga ƙarshe, ina fatan alheri ga ƙaramar hukumarmu ta Malumfashi da jiharmu ta Katsina da ƙasa baki ɗaya.”
__________













