Marigayi Sarkin Labaran Daura: Tunawa Da Mutumin Kirki Mai Zumunci
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
Ina zaune ina binciken tulin hotunan da suke kimshe a faldojin ma’adanata, kawai sai idona ya kai kan wannan hoton, ni da marigayi Sarkin Labaran Masarautar Daura, Alhaji Ibrahim Yaro.
Da ma a kwanakin baya da na kai ziyara Fadar Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Umar Faruk Umar, na gana da ɗan marigayin, Alhaji Usman Ibrahim Yaro, wanda kuma shi ne ya gaje shi a wannan sarauta. A yanzu haka shi ne Sarkin Labaran Masarautar Daura na yanzu.
A lokacin da muke tunawa da Marigayin, mun tattauna al’amura sosai dangane da shi. Ya tuno lokacin da marigayin yake raye, yadda ya ɗauki Ƙungiyar Gizago da muhimmanci, a matsayinsa na Uban Ƙungiya.
Babu shakka nakan tuna kyawawan halayensa na himma da son zumunci. A matsayinsa na jajirtaccen Uban Gizagawa, marigayi ya yi hidima mai tarin yawa na jaddada zumunci da ‘yan uwantaka. Nakan tuna yadda a duk lokacin da aka kira taro, marigayin kan cika motarsa da mai, ya ɗauki ayarinsa tun daga Daura, ya halarci taron.
Muhimman taruka biyu ne ba zan mance da su ba, inda marigayin ya halarta kuma ya yi hidima mai yawa. Na farko shi ne taron Kaduna, wanda aka gudanar a Arewa House a shekarar 2010 da kuma taron Goron Sallah, wanda aka gudanar a Funtuwa, a shekarar 2011. Ba zan mance ba, a Funtuwa ne ma muka ɗauki wannan hoton.
Duk wani Bagizage da ya kwana cikin Ƙungiyar Gizago, ya san irin ƙima, daraja da mutuncin marigayi Sarkin Labaran Masarautar Daura, Alhaji Ibrahim. Babu abin da muka sani a kansa, daga alheri sai alheri, sai zumunci da mutunci.
A yau da nake tuna wannan bawan Allah, ni Bashir Yahuza Malumfashi, Gizago, a madadin ɗaukacin Gizagawan Zumunci da ke faɗin duniyar nan, muna addu’a: Allah ya ji ƙan Sarkin Labaran Masarautar Daura, Alhaji Ibrahim Yaro. Allah ya sanyaya makwancinsa, ya jaddada masa rahama. Allah ya ba shi ladar zumuncinsa da muke tunowa a yau. Amin-Summa-Amin!
_______________













