Wakilin RFI HAUSA Malam Kabir Yusuf Ya Rasu

A safiyar yau Laraba, 26-12-1445 = 03-07-2024, Allah Ya yi wa Malam Kabir Yusuf rasuwa.
Kafin rasuwar tasa, Malam Kabir shi ne wakilin Sashin Hausa na RFI HAUSA na Abuja. Ya rasu yana da shekara 63.
‘Yan uwa da abokan arziƙi da suka san marigayin, sun ba da shaidar cewa shi mutum ne mai addini kuma na ƙwarai. Amininsa, Malam Uwaisu Abubakar Idris wanda shi ma ɗan jarida ne kuma wakilin Sashin Hausa na Muryar Jama’ar Jamus da ke Abuja, ya bayyana cewa tare suka yi Hajjin Bana. Ya ce kafin dawowar sa Najeriya, sai da ya ba shi WASIYYA, inda ya ce yana jin ba ya lafiya, yana ganin alamar ya kusa barin duniya. Allahu Akbar.
Muna roƙon Allah Ya ji ƙan shi da rahama. Mu da muka rage, Allah Ya sa mu cika da imani, idan namu lokacin ya yi.













