HAƊIN KAI: SHAWARA TA MUSAMMAN GA ƊAUKACIN MARUBUTAN HAUSA
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
A yau, kowa shaida ne yadda harshen Hausa da adabinsa suka shahara kuma suka karaɗe dukkan duniya. Haka kuma kowa shaida ne yadda harshen da masu harshen suke ba da gagarumar gudunmowa a dukkan sassan rayuwar al’umma, waɗanda suka haɗa da ayyuka da sana’o’i, ilimi, tsaro, noma, nishaɗantarwa, watsa labarai, wayar da kai, addini da sauransu.
Sai dai kuma duk da wannan ɗaukaka ta harshen, amma an bar MARUBUTAN HAUSA a baya. Marubutan Hausa sun zama gugar yasa, sun zama tattaki, duk kuwa da cewa a kullum da bazarsu ake rawa. A fannin ilimi, da littattafansu ake amfani a jami’o’i da kwalejijin ilimi. A finafinai, da ayyukansu ake bugun gaba. Za ka ga malamin jami’a ya zama gangaran, albarkacin marubutan Hausa. Za ka ga furodusa, darakta da aktoci sun samu shahara da tarin dukiya, duk albarkacin marubutan Hausa. Amma abin takaici, su marubutan suna durƙushe, an mayar da su tamkar mabarata. Wannan shi ake kira, kura da shan bugu, gardi da amshe kuɗi.
Kuma wannan lalacewar, tana faruwa ne ga MARUBUTAN HAUSA na wannan zamani kaɗai. Muna sane a tarihi, yadda marubutan dauri suka samu gata da tarairaya daga gwamnatocin zamaninsu, da ma sauran al’umma. Haka kuma a wannan zamanin, muna ganin yadda MARUBUTAN INGILISHI ke samun tagomashi da kula ta musamman daga gwamnati da ma al’ummar duniya. To ga tambaya: Shin me ya sa marubutan Hausa na wannan zamani ke fuskantar wannan ƙalubale?
Babbar amsa ita ce, RASHIN HAƊIN KAI. A yau, marubutan Hausa suna da ƙungiyoyi barkatai amma na banza. Ƙungiyoyi ne na je-ka-na-yi-ka, tarin tsintsiya babu shara. Ƙungiyoyi ne da suka yi kama da kumfar kogi, sai yawan afki amma babu wani alfanu.
Haka kuma, wani dalilin da ke haifar mana da koma baya shi ne, SON KAI da NINANCI da HASSADA da ƘYASHI. Ba sai na fassara ma’anar waɗannan matsaloli ba ga dukkan wani marubuci da marubuciyar Hausa. Domin kuwa ruwa ya daɗe yana kwarara, ƙasa tana shanyewa. To yanzu, ina mafita?
Babu shakka, madamar marubutan Hausa suna son gyara lamarinsu, to ya zama dole su yi karatun-ta-natsu, domin fitar da jaki daga duma. Ya zama dole a magance, waɗancan matsaloli da na zayyano a baya. Lamari ne mai sauƙi kuma mai wuya. Mai sauƙi ne idan muka ɗaura niyya da kyakkyawar manufa. Kuma lamari ne mai wuya, idan ba mu shirya kawo gyaran ba da gaske.
Domin samar da HAƊIN KAI, ya kamata mu yi amfani da wannan taro na bana, wajen kafa GAGGARUMAR ƘUNGIYAR MARUBUTAN HAUSA TA NAJERIYA. Wacce za ta zama babbar uwa ga dukkan marubutan Hausa kuma ta zama uwa ga dukkan sauran ƙungiyoyin marubuta da ke akwai a sassa daban-daban a faɗin ƙasa.
Dole marubuta su haɗa kai a ƙarƙashin wannan ƙungiya. Kuma a samar mata da JAJIRTATTUN SHUGABANNI, waɗanda ya kamata a zaƙulo su daga sassan jihohinmu gaba ɗaya.
Tun yanzu, a shirye-shiryen nan na ranar taron Jigawa, a fara tattauna samar da wannan ƙungiya, a samar da shugabannin riƙon ƙwarya, waɗanda za su jagorance ta zuwa ga nasara, kafin ta kafu. A nan, ina ba da shawara, a miƙa shugabancin riƙo ga jajirtacce, mai ƙaunar adabin Hausa da marubutan Hausa – FARFESA ABDALLA UBA ADAMU. Sannan a sama masa mataimaka daga marubuta maza da mata daga jihohinmu daban-daban.
Ina da tabbacin, muddin muka samu wannan ƙaƙƙarfar ƙungiya kuma muka cire son kai, muka cire ninanci, muka cire ƙyashi da hassada daga zukatanmu, wallahi MARUBUTAN HAUSA sai sun zama abin kwatance a duniya baki ɗaya.
Ina fata da roƙon Allah ya sa mu duba wannan shawara, mu yi wa kanmu ƙiyamullaili, domin kawo gyara ga lamarinmu, yadda mu ma za mu amfana daga baiwar da Allah ya ba mu.
Allah sa mu dace, ya yi mana jagora, Amin.
Wassalam.
Daga ɗan uwanku a Alƙalami da Takarda,
Bashir Yahuza Malumfashi
_______________













