58: ALHAMDU LILLAH

•••••
A yau, Alhamis 17-11-1446 (Hijiriyya), 15-05-2027 na cika shekara 58 a duniya. Wannan ƙasida, godiya ce ga Allah (swt) da ya ba ni rayuwa.
•••••
Assalamu alaikum, iyayena.
Na haɗa da abokai da dukkan zumaina.
Godiya nake ga Allah maƙagina.
Wanda shi ke tafiyar da ɓargona.
Salati da sallama gun masoyina.
Gwarzon Khadijatu, baban Nana.
Farin gani, Jakada Muhammaduna.
Kullum begenka na nan a ƙirjina.
‘Yan uwana, ga godiyar ƙauna.
Haɗi na da ku, kuna sona.
Na yo zance, kun yabo guna.
Duk motsi, addu’a ce kuke kaina.
Murna kuke da alheri ya zo guna.
Mazanku da matanku, tabbacina.
Masoya ne na haƙiƙa, ya zumaina.
Allah ya biya ku, addu’a daga guna.
Yai maku rahama, shi ne muradina.
Mu zam tsira gaban Allah, gwanina.
Wancananku, su ne magabtana.
Ba su son alheri, ya zo guna.
Ƙyale shawarakai, ba sa gabana.
Na ci, na sha, Allah ne garkuwana.
Ni Bashir, na gode Allah rayuwana.
Yau ga ni hamsin, shekaruna.
Ƙaro takwas, ɗora bisana.
58, shekarun haihuwana.
Na sha miya, na taune ƙashina.
Sai hamdala ga Rabbil alamina.
Allah ƙaro ni lafiya, ƙasussana
Da imani, dukkan gaɓoɓina.
•••••
Tammat
_______________
© Bashir Yahuza Malumfashi
Alhamis 17-11-1446 (Hijiriyya)
15-05-2025 (Miladiyya)












