TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNKASA MALUMFASHI DA KEWAYE (4)
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

A wannan muƙala mai samfurin rahoto, a yau za mu ɗora da abin da ya biyo bayan muƙalar da Shugaban Hukumar Sufuri ta Jihar Katsina, Malam Haruna Musa Rugoji ya gabatar, wacce ta yi tambihi game da matsayin Musulunci dangane da Soshalmidiya.
Shin mene ne ya biyo bayan muƙalar tasa? Ta’aliƙi ne mai ɗaukar hankali da fadakarwa daga bakin Dokta Aminu Garba Waziri.
√ Wane Ne Dokta Aminu Waziri?
Dokta Aminu dai ɗaya ne daga cikin jajirtattun masu kishin al’umma da Allah ya albarkaci Malumfashi da su. Babu wai, bisa la’akari da tarihinsa, shi mutum ne da bai sa komai ba a gabansa face yadda zai rufa wa kansa da iyalansa da ma al’umma asiri.
Mutum ne shi mai himma da daraja harkar ilimi, dalili ke nan ma ya saita dugadugansa bisa neman ilimi da ilimantarwa, wanda a halin yanzu shi cikakken mamallakin Digirin-Digirgir (phD) ne kuma yana kan hanyar zama Farfesa. Fitaccen masanin harkokin safiyo da fuloti, malamin jami’a, ɗan siyasa kuma ɗan kasuwa, wanda a yanzu haka yake shugabantar kamfanin harkokin fulotai da kasuwancinsu, na AG Waziri &Co.
A fannin siyasa kuwa, Dokta Aminu ya taɓa zama Sakatare a Ƙaramar Hukumar Malumfashi. Ya taɓa zama Shugaban Ƙaramar Hukumar Malumfashi. Ya taɓa zama Mataimaki Na Musamman ga Shugaban Majalisar Tarayya. Ya taɓa zama Sakataren Dindindin a Jihar Katsina, kamar kuma yadda ya taɓa zama Babban Sakataren Hukumar Agajin Gaugawa ta Jihar Katsina (SEMA). Ta ɓangaren wasannin motsa jiki kuwa, mutum ne shi mai buga Kwallon Dawaki (Polo).
Ta fuskar halayya kuwa, Dokta Aminu Waziri ya samu kyakkyawar shaida, a matsayin mutum mai sauƙin kai, mai zumunci kuma mai taimakon mabuƙata. Ga duk wanda ya yi mu’amala da shi, da wuya ka ji ya ambata wani aibu daga gare shi, idan ka cire ajizancin da ake samu daga kowane ɗan Adam.
√ Ta’alikin Doka Aminu Waziri
Kamar yadda bayani ya gabata, Malam Haruna Musa Rugoji ne ya gabatar da muƙala mai taken, “Mahangar Musulunci Dangane Da Soshalmidiya.” A matsayinsa na mai ta’aliƙi, Dokta Aminu ya buɗe da addu’a, inda ya ci gaba da bayani tare da fashin baƙi dangane da al’amuran Soshalmidiya.

Dokta ya bayyana cewa a halin da ake ciki, zamani ya kawo intanet kuma al’umma musamman matasa sun rungumi Soshalmidiya. Ya kawo ƙididdiga daban-daban, inda yake tabbatar da yadda a duk shekara, yawan al’ummar da ke amfani da kafar Intanet/Soshalmidiya ke ƙaruwa. A misali, ya ce a shekarar 2024, an samu ƙiyasi da ƙididdigar da ke shaida cewa akwai matasa, masu shekaru 16 zuwa 30 kimanin miliyan 16.2 da ke amfani da kafafen sadarwa na zamani. Ya ce kuma a kullum adadin ƙaruwa yake.
Dokta ya ce babu makawa, amfani da Soshalmidiya ya zama dole ga al’umma, domin rayuwa ta karkata gare ta. Sai dai kuma ya jawo hankalin al’umma da su bi al’amarin cikin tsari da abin da ya dace da umurni da hanin Allah da Manzonsa (saw). Ya ce iyaye da malamai da shugabannin al’umma suna da babbar rawar da za su taka, wajen yi wa matasa jagoranci, domin ganin an riƙa amfani da kafafen sada zumunta yadda ya dace.
Ya ce, a matsayin mutum na Musulmi, ya tabbatar da ya nemi ilimin addini da na mu’amala, yadda zai riƙa tu’ammali da kafafen yadda ya dace da kuma ɗaukar abin da zai amfane shi duniya da lahira, tare da kauce wa faɗawa cikin abin da zai cutar da shi da imaninsa. Wata babbar shawara da ya bayar ga al’umma ita ce: “A duk lokacin da muka shiga intanet, to mu yawaita yi wa Annabi Muhammadu (saw) salati.” Ya ce akwai fa’ida mai yawa ga haka, inda mutum zai samu lada kuma ya samu jagorar aikata abubuwa masu muhimmanci a waɗannan kafafe na sada zumunta.
Haka kuma, ya ja hankalin cewa, wani babban ƙalubale da ake fuskanta a kafafen sada zumunta, shi ne yaɗa hotuna da bidiyo masu lalata ko bayyana tsiraici. Wannan abu ne da ya saɓa wa koyarwar Musulunci. Allah (SWT) ya ce: “Ka ce wa muminai su rage kallonsu kuma su kiyaye farjinsu, hakan shi ne mafi tsabta a gare su.” (Suratun Nur: 30). Wannan umarni yana nuna muhimmancin kiyaye kallo da bayyana sassan jiki a bainar jama’a.

Game da mu’amalar rayuwa kuwa, haƙiƙa Musulmi ya kamata ya kasance wakili na alheri a ko’ina, har da kafar intanet. Dandalin sada zumunta na iya zama wata hanya mai kyau ta yaɗa addini da kyawawan halaye idan aka yi amfani da ita bisa adalci da tsoron Allah. Manzon Allah (SAW) ya ce: “Duk wanda ya ga wani mummunan aiki a cikin al’umma, to ya gyara da hannunsa, idan ba zai iya ba, da bakinsa, idan har hakan ma ba zai iya ba, to ya ƙi abin a zuciyarsa…” (Muslim).
Wajibi ne ga Musulmi ya lura cewa, duk abin da yake yi, mala’iku na rubutawa. Wallafawa ko yin comment a kan wani abu na laifi, ko kallon abubuwa haram, duk suna cikin abin da ake rubutawa. Allah ya ce: “Babu wata kalma da zai faɗi sai akwai mai lura da rubutawa a gabansa.” (Surah Qaf: 18). Wannan yana nuna cewa duk abin da ake aikatawa a kafar sada zumunta zai bayyana a ranar hisabi.
Daga ƙarshe, Dokta Aminu Waziri ya shawarci mutane da cewa, yana da kyau Musulmi ya mayar da Soshalmidiya matsayin wata hanya ta neman lada, ta hanyar yaɗa ilimin addini, ingantattun hadisan Manzon Allah, da karfafa zumunta cikin gaskiya da amana. “Duniya wata rana za ta ƙare, amma duk abin da aka aikata za a sake ganinsa a gaban Allah. Don haka, kada mu bari kafar da za ta iya zama hanya ta alheri ta koma hanyar da za ta kai mu ga halaka. Allah ya shiryar da mu baki ɗaya.” In ji Dokta Waziri, a yayin da yake ƙarkare ta’aliƙinsa.
In sha Allahu, a rahoto na gaba, za mu kawo maku jawabi na musamman daga bakin Sardaunan Matasan Galadiman Katsina, Malam Abdul’aziz Ibn Abdul’aziz.
_______________
Bashir Malumfashi, shi ne Editan Mujallar Taskar Gizago (online)













