SASSANYAN AMINCI (3)
(Diwanin Bashir Yahuza Malumfashi)

_______________
17
Mu matsa gaba don mu gane,
Tsatson Manzo kar mu gune,
Shalikh shi ma kaka ne,
Abir shi ya wuce ƙanƙane,
Tushe na Manzo babba.
18
Salsala da salamar girma,
Manzonmu ɗan mai girma,
Mai kakanni masu girma,
Ga Faligh uba mai himma,
Jigo ne shi ba wai ba.
19
Ra’u a cikin lissafi,
Sarugh mai takobin kaifi,
Nahur mutum mai ƙarfi,
Azur shi ba ya tsafi,
Sun shuɗe ba tababa.
20
Matso ku zo ga gwarzo,
Kakan Muhammadu Manzo,
Sahihi shi ma Manzo,
Mai bautar Allah da ƙwazo,
Ibrahim jigo babba.
21
A yanzu reshen ya matso,
Na kakanni da na tsatso,
Isma’il shi ya kutso,
Iyayen Manzo abin so,
Almustapha ba wai ba.
(Za Mu Ci Gaba)
_______________
Akwai bayin Allah da suke taimakawa domin ganin nasarar an wallafa wannan Diwani, saboda ƙaunarsu ga Fiyayyen Halitta. Don haka, muuna addu’a ta musamman ga waɗannan bayin Allah (Masoya Manzon Allah – Saw), da suke taimaka wa wannan aiki:
1-Alhaji Jibrin Sama’ila (Jibson).
2-Injiniya Tukur Tingilin
3-Malam Labiru Musa Kafur
4-Malam Haruna Musa Rugoji
5-Dr. Aminu Waziri
6-Abdulaziz Abdulaziz
7-Zainab Ahmad Mohammed
Allah ya saka maku da mafificin alheri, ya ƙara mana ƙaunar Manzonsa (saw), ya sa muna cikin cetonsa, Amin!
_______________













