SASSANYAN AMINCI (2)
(Diwanin Bashir Yahuza Malumfashi)

__________
12
Yau za ni waiwayi baya,
Sanin asali da sanayya,
Tarihi ba jayayya,
Manzonmu kyan halayya,
Asalinsa bai ɓoye ba.
13
Tushensa Annabi Adamu,
Hauwa’u Sarauniyarmu,
Su ne jigon zuri’armu,
Manzo Muhammadu namu,
Yai gargaɗin hana zamba.
14
Na biyunsu Annabi Shisu,
Sannan akwai Anushu,
Da Ƙinan sanya a cikinsu,
Mahlail, biyar ɗan uwansu,
Tushe na Manzo babba.
15
Sauran akwai su da dama,
Idrisu a hannun dama,
Mutushalih gwarzon fama,
Na tara, Lamak mai girma,
Sun zamani ba wai ba.
16
Annabi Nuhu mun san shi,
Ya sha daga zamaninshi,
Akwai Sam, can bayanshi,
Arfakhshaz yana a sashi,
Kakanni ne ba wai ba.
(Za Mu Ci Gaba)
__________
Akwai bayin Allah da suke taimakawa domin ganin nasarar an wallafa wannan Diwani, saboda ƙaunarsu ga Fiyayyen Halitta. Don haka, muuna addu’a ta musamman ga waɗannan bayin Allah (Masoya Manzon Allah – Saw), da suke taimaka wajen wannan aiki:
1-Alhaji Jibrin Sama’ila (Jibson).
2-Injiniya Tukur Tingilin
3-Malam Labiru Musa Kafur
4-Malam Haruna Musa Rugoji
5-Dr. Aminu Waziri
6-Abdulaziz Abdulaziz
7-Zainab Ahmad Mohammed
Allah ya saka maku da mafificin alheri, ya ƙara mana ƙaunar Manzonsa (saw), ya sa muna cikin cetonsa, Amin!
__________













