SASSANYAN AMINCI (1)
(Diwanin Bashir Yahuza Malumfashi)

__________
Gabatarwa:
A yau Alhamis, 11 ga Rabi’ul Auwal, 1447 Hijiriyya, wacce ta yi daidai da 04 ga Satumba, 2025 Miladiyya. A yau muke murnar zagayowar ranar da aka haifi Manzon Allah, Muhammadu (saw). Daga yau za mu fara wallafa wannan diwani, mai ƙunshe da baitoci dubu ɗaya cur, na begensa – Sallallahu Alaihi Wasallam.
Akwai bayin Allah da suke taimakawa domin ganin nasarar an wallafa wannan Diwani, saboda ƙaunarsu ga Fiyayyen Halitta. Don haka, muuna addu’a ta musamman ga waɗannan bayin Allah (Masoya Manzon Allah – Saw), da suke taimaka wajen wannan aiki:
1-Alhaji Jibrin Sama’ila (Jibson).
2-Injiniya Tukur Tingilin
3-Malam Labiru Musa Kafur
4-Malam Haruna Musa Rugoji
5-Dr. Aminu Waziri
6-Abdulaziz Abdulaziz
7-Zainab Ahmad Mohammed
Allah ya saka maku da mafificin alheri, ya ƙara mana ƙaunar Manzonsa (saw), ya sa muna cikin cetonsa, Amin!
GUDUNMOWA:
Al’ummar Allah, ga duk mai son saka jarinsa a wannan aiki, ƙofa a buɗe take. A tuntuɓi Bashir Yahuza Malumfashi a wannan layin waya:
+234 8065576011
_______________
1
Bismillah na ɗau niyya,
A cikin ladabi da biyayya,
Zan tsara baitin soyayya,
Ga halittar Allah fiyayya,
Ban ɗaura yin wasa ba.
2
Ya Allah ka ba ni basira,
Ka raba mu da dukkan asara,
Zan yabon mai hana fitsara,
Sha yabo tuli ya sahara,
Shugaban muƙami babba.
3
Assalamu alaika Nabiyyu,
Shugaban dukkan anbiya’u,
Alhashimi, Ƙuraishiyyu,
Kai ne badadin Hayyu,
Kai ke da haske babba.
4
A halittu ba ka da tamka,
Kyakkyawa ko ba wanka,
Babban danni mai tanka,
Girmanka ya wuce jinka,
Sirri na Allah babba.
5
Kai Maliya ka wuce gulbi,
Tsarki gare ka a ƙalbi,
Aikinka gyaran ƙalbi,
Tauraro ka wuce halbi,
Shugaba kake ba wai ba.
6
Manzo muna ƙaunarka,
Muna ta ƙin mai ƙinka,
Mun gane duk girmanka,
Mun san da duk tsarkinka,
Mai sonka ba zai taɓe ba.
7
Ɗan Amina ka wuce karo,
Ran Litinin kag gangaro,
Babu kuka ba wani ɓaro,
Sai murmushi ka ƙaro,
Murna ga dangi babba.
8
Na Khadijah babban gwarzo,
Ga baituka naka murzo
Bisa izza duka naka furzo,
Maƙiyanka duk zan gurzo,
Bauta nake ba wai ba.
9
Ka fi ruwan sanyi a bazara,
Kyauta wurinka ba tazara,
Kyan ɗaki sai da azara,
Murmushi kullum ka zizara,
Kai ke da hairi babba.
10
Ka fi zuma zaƙi ko madara,
Kai kake izza ga mahara,
Ja’irai sun zam a makara,
Ba su da riba sai dai takura,
Kai ke da turke babba.
11
Haƙuri ka zarce wa damo,
Ba ka murna da ƙanƙamo,
Mai ƙaunarka ya kandamo,
Alheri za ya fantamo,
Ba zai rasa yin dace ba.
__________
© Bashir Yahuza Malumfashi,
11-03-1447 (Hijiriyya)
03-09-2025 (Miladiyya)
(Za mu ci gaba)













