BAKIN JAƁA (1)
(Labarin Cin Amana)
Daga Bashir Yahuza Malumfashi
_______________
Gabatarwa:
Wannan labari ne na gaskiya a haƙiƙa, wanda ya taɓa faruwa. Kodayake an sarrafa shi a siga ta daban da ainihin yadda ya faru. An jirkita sunayen waɗanda labarin ya faru da su, da sunayen garuruwa da wuraren da abin faru. Haka kuma an ƙara wasu abebaɗai, a matsayin gishirin da zai zaƙaƙa miyar labarin. Amma tabbas, akwai darussan rayuwa abin dubawa da yawa a labarin.
_______________

Jummalo ‘Yarkaka tana zaune a bakin gado, ta rungume kumatunta cikin tagumin takaici. Abin duniya ya gama dagule mata, ta rasa tudun dafawa. Caraf sai ta ɗauki wayarta samfurin Samsung, ta fara daddanawa.
“Kash! Ashe ma ba ni da Data.” Abin da ta faɗa ke nan bayan ta buga wani uban tsaki wanda ya yi kama da na wata gawurtattar tsaka. Nan da nan ta ƙara shiga cikin wani takaicin. Ƙwaƙwalwarta ta cunkushe da tunani, gami da zullumi iri-iri.
“Wohoho! Wannan wace irin rayuwa ce? Shin wane laifi na yi wa Allah da ya jarabce ni da waɗannan…”
‘Yarkaka, ba ta ida kammala jimlar ba sai ta ji saukar zazzafan hawaye a kumatunta. Kafin ta ankara, har ta fara kuka, gami da shessheka.
Cikin ƙanƙanen lokaci, ƙwaƙwalwarta ta shiga zarabtu da kai komo bisa abubuwan da suka yi ta faruwa da ita a rayuwa. Tunanin nata ya gawurta, inda ya riƙa shigar giza-gizai. Da zarar ta tuno da wannan abin takaici, sai zaren tunanin ya tsinke. Kafin daƙiƙa ɗaya, sai kuma wani sabon zaren takaicin ya sake saƙa kansa a zuciyarta. Ba za ta ida shi ba, sai kuma wani ya sake yin kutse.
Jidali noman Barka – da baya, da baya ya zoƙale. Wannan shi ne yanayin da ‘Yarkaka take ciki. Ba ita ta gushe ba cikin gogoriyon tunani, har sai da ta ɗauki kanta zuwa rayuwarta ta makarantar boko. Ta koma baya yadda ta yi auren fari, wanda dudu bai wuce wata biyar ba suka sallama wa juna da mijinta. Ta yi ninƙaya cikin nazarin yadda wannan aure nata ya samar mata da haihuwar yaro guda ɗaya tilo, da yadda ta sha wahalar rainonsa a gidan iyayenta.
Haka kuma ta ci gaba da zancen zucci, yadda ta ƙaƙara ta koma makaranta domin karatun gaba da sakandare . A nan ne tunani ya gitto da hoton yadda rayuwarta ta samu tagomashi a Kwalejin Ilimi ta Zariya. Ta tunano irin ƙawaye da abokai da ta yi mu’amalar ɗalibta da su.
Rayuwa tamkar hankaka ce, mai launukan fari da baki. A daidai lokacin da ‘Yarkaka take kan tunano rayuwar makaranta, sai kuma zaren tunanin ya katse, wani sabo ya tsiro. Ta hasko yadda ta yi kutse ta tsunduma cikin ƙungiyoyin masu harkar shirya finafinan Hausa. Nan ma ba ta gushe ba sai da ta ƙarƙare komai…
A haka kuma ta koma tunanin yadda ta samu kanta a duniyar zawarci. Irin yadda ta yi faɗi tashi da manema – na ƙarya da na gaskiya. Sannu a hankali har tunanin nata ya ƙaraso zuwa wannan yanayi da take ciki, inda sabon auren da ta yi ya mutu cikin ƙanƙanen lokaci.
“To, ni yanzu ta ina zan fara kuma ina na nufa? Na ƙarar da komai a wajen auren nan, wanda ya kawo ƙarshe cikin wata biyar. Na yi zaton miloniya na aura… ashe hangen dala na yi.”
“Ke Jummalo!” Mahaifiyarta ce ta ƙwala mata kira, a lokacin da ta ga yanayin da take ciki na hawaye tare da maganganun da suka yi kama da sambatu.
“Me ya faru da ke ne?” Mahaifiyar tata ta ci gaba da tambayar jin bahasi. “Kada fa ki je ki halaka kanki. Shin a kanki ne aka fara mutuwar aure? Wa ya gaya maki ƙarshen duniya ke nan?”
Jummalo saurarenta kawai take yi amma ta kasa furta komai. Ta dai ƙura wa mahaifiyarta hajar mujiya, a yayin da ƙwalla ke ta malala a kumatunta.
(Za mu ci gaba)
_______________














😂