• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, January 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

KTSTA: HARKAR SUFURI A HANNUN GWANI (3)

RAHOTON MUSAMMAN

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
August 13, 2025
in Gizago
0
KTSTA: HARKAR SUFURI A HANNUN GWANI (3)

Malam Haruna - Gwani a Harkar Sufuri

24
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

KTSTA: HARKAR SUFURI A HANNUN GWANI (3)

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (8)

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (8)

January 13, 2026
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (7)

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (7)

January 9, 2026
Malam Haruna – Gwani a Harkar Sufuri

 

                            •••••••

A wannan rahoto kashi na uku, za mu kammala bayani ne game da taƙaitaccen tarihin Shugaban Hukumar Sufuri ta Jihar Katsina (KTSTA), Malam Haruna Musa Rugoji, kamar yadda muka faro a rahoto kashi na biyu.

Tarihinsa ba zai cika ba, sai mun waiwayi baya, yadda ya samu ƙwarewa a harkar sufuri, tun ma kafin ya samu kansa a wannan muƙami a KTSTA.

A can baya, ya yi gwagwarmayar tuƙin babbar mota (DAF), mallakin mahaifinsa. Malam Haruna ya shahara kuma ya yi tashen da duk sai da kowace kasuwar shanu da ke Arewa aka san shi. A lokacin, ana yi masa lakabi da Haruna D.K. A wancan lokaci, saboda jajircewa da ƙoƙarinsa a fagen tuƙi, cikin kwana biyu yake zuwa da juyowa ga Legas daga Arewa; alhali wasu direbobin sai sun yi mako guda a kan hanya.

Malam Haruna Musa Rugoji

Baya ga harkar sufuri, Malam Haruna kuma ɗan siyasa ne – amma mai ingantaccen ra’ayi – bai yarda da siyasar ko-a-mutu-ko-a-yi-rai ba. Ba ya fitowa takara kai tsaye, sai dai idan al’umma sun tsayar da shi don ƙashin kansu. Dukkan yunƙure-yunkuren da ya yi a baya na takarar Ciyaman ko Ɗan Majisar Jiha, wasu ƙungiyoyin mutane ne suka buƙaci ya tsaya, domin sun aminta da cewa zai kawo gyara a hidimar al’umma.

Hannu ɗaya, masu iya magana sun ce ba ya ɗaukar jinka. A matsayinsa na ƙwararre a fannin kasuwanci da sufuri, Malam Rugoji yana cikin cibiyoyi da ƙungiyoyin ƙwararru daban-daban. Shi mamba ne a waɗannan ƙungiyoyi, makarantu da cibiyoyin ƙwararru: Institute of Corporate Executive of Nigeria da Institute of Transport Administration of Nigeria da Chartered Transport – The Council for the Registration Transportants in Nigeria da Institute of Industrialists and Corporate Administrators of Nigeria da Charted institute of Transport and logistics London, UK da Fleet Management in Road Transport Operations by the Nigerian Institute of Transport Technology (NITT).

Wani al’amari da ke taimakon Rugoji a rayuwa shi ne, yadda Allah ya ba shi ilimin addinin Musulunci, ga shi kuma da hikimar magana. Yana da zurfi da kaifin tunani, a yayin ɗaukar wani mataki ko zartar da al’amari. Ya iya magana, karatu da rubutu da yaruka uku manya – Hausa, Ingilishi da Larabci. Duk inda zai shiga a duniya, ba ya bukatar tafinta, domin duk runtsi za a iya samun mai magana da ɗaya ko dukkan waɗannan yaruka uku.

Malam Haruna a bakin aikinsa a ofis

Haka kuma ya iya lissafi da ƙididdiga. Yana da ɗabi’ar bin diddigin matsala da gano hanyoyin warware ta cikin sauri. Yana da daraja lokaci a dukkan lamurransa. Yana da biyayya ga shugabanni, yana daraja doka da oda da ƙa’idojin hukuma ko waɗanda aka gindaya domin maslahar al’umma. Yana daraja mutane manya da na ƙasa da shi kuma ya iya aiki a ƙungiyance tare da ba kowa haƙkinsa.

Wani babban tambari da ya bayyana a cikin halayensa, wanda duk mutumin da ya yi mu’amala da shi zai shaida shi ne, shi mutum ne mai tsananin kwatanta gaskiya da adalci. Mutum ne mai ƙoƙarin cika alƙawari – kaifi ɗaya. Ba ya da nuƙu-nuƙu, idan zai yi abu to zai yi, idan kuwa bai natsu da abu ba, to ba zai yi ba.

Yaba kyauta, an ce tukwici! Malam Rugoji ya samu kyaututtuka da lambobin yabawa da yawa. Misali, ya samu Takardar Yabo ta Ƙasa daga Fadar Shugaban Ƙasa (National Productivity Order of Merit Award), wacce Shugaban Ƙasa Janar Muhammadu Buhari (Allah ji ƙan shi ) ya miƙa masa a ranar 10 ga Mayu, 2022. Ya taɓa samun Takardar Yabo ta Musamman (sau biyu) daga Majalisar Dokoki ta Jihar Katsina, a ranar 30 ga Maris, 2022 da kuma wacce aka ba shi a ranar 9 ga Janairu, 2023 saboda yabawa da ƙwazonsa a aiki. Haka kuma ya samu wata karramawar a matsayin Gwarzon Hadimin Al’umma a Fannin Sufuri a Jihar Katsina da Ƙasa Baki Ɗaya (2018 – 2019). Sauran karramawa da yabo daga ƙungiyoyin al’umma, makarantu da cibiyoyi kuwa, ba za su lissafu ba cikin sauri.

A hagu, Malam Haruna ne tare da Injiniya Muntari Sagir Malumfashi, yayin da Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari ya karrama shi, a shekarar 2022

Malam Haruna Musa Rugoji, shi mai sarauta ne a Fadar Galadiman Katsina Hakimin Malumfashi, Justice Saddik Abdullahi Mahuta, OFR. Shi ne Ubandawakin Galadiman Katsina. Yana da kyakkyawar shaida da aminci daga Mai Girma tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, CFR da Farfesa Y. Haruna na Jami’ar Abubakar Tafawa Ɓalewa University of Technology Bauchi, CSP. Saleh M. Abdulhameed.

A rahoto na gaba, kashi na 4, in sha Allahu za mu duba irin wainar da Malam Rugoji yake toyawa a wannan hukuma mai albarka ta KTSTA, a matsayinsa na shugaba. Shin yaya ya samu ma’aikatar a 2018 kuma zuwa yanzu yaya take?
_______________
Bashir Malumfashi, shi ne Editan Mujallar Taskar Gizago (online)

Previous Post

Nigeria 2027: The Best Way to Defeat President Tinubu

Next Post

TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNKASA MALUMFASHI DA KEWAYE (6)

Related Posts

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (8)
Gizago

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (8)

January 13, 2026
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (7)
Gizago

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (7)

January 9, 2026
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (6)
Gizago

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (6)

January 6, 2026
Next Post
TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNKASA MALUMFASHI DA KEWAYE (6)

TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNKASA MALUMFASHI DA KEWAYE (6)

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

UNDP Partners Kaduna Ministry to Build Peace in the State

UNDP Partners Kaduna Ministry to Build Peace in the State

September 20, 2023
TEARS AND BLOOD

TEARS AND BLOOD

November 4, 2024

Huɗubar Jumu’a Daga Limamin Masallacin Unguwar Tumbu-Madallah

July 14, 2023
Tribute to Cultural Broadcaster: Muhammad Salissou Hamissou

Tribute to Cultural Broadcaster: Muhammad Salissou Hamissou

February 24, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation
  • Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco
  • Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

January 15, 2026
Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.