Daga Sharif Almuhajir
Jiya na bi gefen filin Idi, na ga plazar wani aboki na tayi kaca-kaca da aikin barayi ma su dibar ganima a Kano, na tabbata ya yi hasara ta fi miliyan 300 a rushe-rushen nan da ake yi da sunan gyara, kuma na ga yadda mutane suka shiga shagunan mutane suka balle kofofi suka yi musu sata ta wilaknci, gaskiya har sai da hawaye ya fito daga ido na. Har sai da na ce a zuciya ta, Wai shin garin babu jami’an tsaro ne?
Haba jama’ah, ita Gonnati fa ta kowace da wanda suka zabe ta da wanda ba su zabe ta ba, da zarar ka zama Gomna shikenan kowa ya zama na ka. Na dauka ko da a wata kasa ne aka cutar da mutanen Kano haka, Gomnan Kano ne ya kamata ya bi ma su hakkin su, to tayaya zai yi haka da kan shi da umarnin shi. Kwankwaso ne fa ke zuwa har Lagos kwato hakkin mutanen Arewa, tayaya zai yarda ayi haka a Kano?
Mu dauka cewa tsohon Gomna bai kyauta ba kuma ya yaudare su, shi kuma yanzu me yake yi kenan taimakon su? Kuma ma shin akwai wata doka da ta hana Gomna tasarrufi da filayen hukuma ne a duk inda suke, ina dokar ta ke, a kawo ta mu ganta. Menene laifin mutumin da ya yi abunda Gomna ya gaya ma shi.
In dai ka yarda cewa ya wajaba ayi maka biyayya saboda kai Gomna ne, to bai kamata ka ga laifin wadanda suka yiwa wani Gomnan biyayya ba, har ka yi musu mummunan hukunci irin haka ba. Ina laifin ka ware wani fili mai girma, ka ba su kace ga inda na ke so ku zo ku zauna, kafin ka fara tunanin rushe mu su dukiya? Wannan ba daidai ba ne, wannan kuskure.
Ni dai a matsayin danAdam wallahi zuciya ta ta gamsu cewa wannan abun ba daidai bane kuma ba adalci ba ne, kuma na kasa yin shiru saboda tsoron zagi ko cin mutumci, ko saboda kusancin da ke tsakanin mu da wasu mukarrabai, saboda gaskiya na ga cutar da mutane karara wadanda zahirin gaskiya ba su yi wani laifi ba. Sannan saboda me zan yi farin ciki da hasarar da ta samu wani, me ya faru, me ya tare mun?
__
Dokta Sharif Malami ne a Jami’ar Jihar Yobe.
—













