Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Ambaliya: Gwamnan Jigawa Ya Nemi Tallafin Bankin Duniya
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya buƙaci tallafi daga Bankin Duniya domin magance matsalolin ambaliya da ke addabar jihar da kuma tallafi na musamman domin bunƙasa rayuwar matasa a jihar.
Kamar yadda wata takarda da ta fito daga Babban Sakataren Watsa Labarai na Gwamnan, Malam Hamisu Gumel ta bayyana, Gwamnan ya nemi tallafin ne a ranar Larabar da ta gabata, a lokacin da ya kai ziyara ta musamman Ofishin Bankin Duniya da ke Abuja, inda Darakta mai kula da al’amaran bankin a Najeriya, Mista Shubham Chaudhury da ayarinsa suka amshe shi.
Kamar yadda Gumel ya bayyana, Gwamnan ya kai ziyarar ce musamman domin tattaunawa da Bankin na Duniya, ta yadda za a samu shawo kan manyan matsalolin da ke fuskantar al’ummar jihar.
A yayin ganawar, Mista Chaudhury ya yi wa Gwamna Namadi bayani dalla-dalla game da ayyukan bankin da hanyoyin da suke taimakawa, wajen bunƙasa rayuwar al’umma.
A nasa ɓangaren, Gwamnan na Jigawa ya zayyana wa hukumomin bankin irin matsalolin da ke addabar jiharsa ta Jigawa, wanda ya zama tilas su nemi tallafi daga waje. “Jihar Jigawa na fuskantar matsalolin da suka shafi ambaliyar ruwa, wanda a can baya ya lalata hanyoyi, gadoji. Haka kuma ambaliyar ta mamaye gonaki masu murabba’in sama da eka dubu 400. Ga shi a bana, kamar yadda Hukumar Agajin Gaugawa ta Ƙasa (NEMA) ta yi hasashe, ambaliyar za ta ta’azzara. Bisa ga haka, ya zama wajibi mu nemi tallafi daga Bankin Duniya, domin kiyayewa,” in ji Gwamna Namadi.
Gwamnan ya buƙaci bankin na duniya ya taimaka wa jihar a fannonin noma, kiwon lafiya, bunƙasa tattalin arziki da kuma ɓangaren magance ambaliya da kwararowar hamada. Haka kuma ya nemi yadda za a tallafa wa manoma da famfunan ban ruwa masu aiki da hasken rana da hikimomin zamani na bunƙasa noman rani da sauransu.
Da yake maida jawabi, Mista Chaudhury ya ce za su yi nazari na tsanaki game da buƙatun Gwamnan, inda za su duba yadda bankin zai yi haɗin gwiwa da gwamnatin jihar, domin tallafawa yadda ya kamata, domin samun bunƙasa al’umma.













