BAYAN KAMMALA TARON HAƊIN KAN ƘASA A NIJAR, KO ƘUDURORIN TARON ZA SU YI TASIRI?
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••
An kammala Taron Ƙasa a yau Laraba (19-02-2025) a Jamhuriyar Nijar. Ga shawararwarin da taron ya fitar, kamar yadda Shugaban Kwamitin Taron, Malam Tsalha Haladou ya gabatar:
√ An ba da shawarar Gwamnatin Tchani ta kwashe shekara 5 tana Riƙon Ƙwarya, kafin ta mayar da mulki ga Farar Hula.
√ Kwamitin Taron ya buƙaci Nijar ta sauya tsarin amfani da kuɗaɗe ta hanyar mutunta manufofin Ƙungiyar Ƙasashen Sahel (AES).
√ Ya buƙaci a rage yawan ma’aikatun gwamnati domin daƙile almubazzaranci.
√ An buƙaci Gwamnatin Nijar da ta yi watsi da duk wani shiri na tallata auran jinsi (LGBT+).
√ An buƙaci Gwamnati ta sanya ido sosai a kan kafofin yaɗa labarai da na sada zumunta.
√ Taron ya amince da a riƙa tilasta wa duk wani matashi ɗan ƙasa da ya kammala karatunsa yin aikin soja da kuma bautar ƙasa.
__________
Jama’a ko mene ne ra’ayinku a kan waɗannan ƙudurori?











