ZINATU
MATAR GWAMNA
(2)
~~~~~~~
A makon jiya mun tsaya inda aka ce:
“Ƙawarta ce Balaraba ta ƙara tabbatar mata da cewa, lallai ita da samun sauƙin irin waɗannan tsegunguma sai ta yi aure ko kuma wani sanadi ya zo, yadda za ta rabu da iyayenta.”
Ga ci gaba:
~~~~~~~
“Ina son ki gane yanayin al’adunmu da na addininmu,” in ji Balaraba. “A ƙasar Hausa, saboda tasirin addini, yarinya da ta fara girma, ta zama abin tashin hankali ke nan ga iyayenta. Ba za su sake samun kwanciyar hankali ba sai sun ga ta yi aure. Idan ba haka ba kuwa, to, ba za su guje wa maganganu da tsegunguman maƙwabta ba. Idan an yi rashin sa’a kuma sai ki ji ana yi mata yarfe da cewa, ta yi kwantai.”
“To, amma ai ya kamata mu gane cewa duniya ta canza; da da yanzu ba ɗaya ba ne. A zamanin da, kamar yadda muka karanta a tarihi, babu yawan al’umma kamar yanzu, babu talauci da kwaɗayin neman duniya kamar yanzu. Haka kuma, babu ilimin zamani, inda mata da maza za su samu wayewa. To, tun da yanzu duk waɗannan al’amura sun samu canji, me zai hana mu canza mu ma?”
Zinatu na ƙarin bayani ga ƙawarta. Suna tafiya ne bisa titi da maraice. Ga alama, sun dawo daga kasuwar ’Yar Kutungu ne; suna dawowa zuwa gida. Balaraba ta tauna cingam da ƙarfi, ta hura shi bisa leɓɓanta, ta yi balo da shi, sannan ta maida shi cikin baki.
“Kash! Zinatu, kin mance da wani abu ɗaya. Da kike cewa duniya ta canza, wane ne ya canza? Ina son ki gane cewa, mu matasa da ƙananan yara, ’yan zamani; mu ne muka canza, amma su baba da inna da kakanninmu fa, sun canja ne? Don haka, dole ne za mu ci gaba da tafiya haka, suna tafiya, ana canjawa a hankali; har nan gaba yanayinmu da al’adunmu sai su canja.”
“Na yarda da wannan bayanin naki, amma me iyayenmu ke gudu, da suke matsa mana haka game da aure?”
Zinatu ta ci gaba da magana, amma ba ta jira amsar ƙawarta ba, sai ta ci gaba da bayaninta.
“Ina ganin namiji ne ya kamata ya nemi yarinya da aure ko? To, idan bai nema ba fa? Ya kamata yarinya ta je wajen saurayi ne tana roƙon sa, cewa ya zo ya aure ta? Ai wannan zubar da mutunci ne kuma ya saɓa wa al’adar Malam Bahaushe. Ni kam gani nake kamar gajiya aka yi da ni a gidanmu, shi ya sa ake tsangwama ta, wai in yi aure. Duka yaushe na gama wannan makarantar? Ki tuna fa ko jarabawarmu ma ba ta ida fitowa ba.”
Balaraba ta tuntsure da dariya, har tana tuntuɓe. Takalminta ne ya ci karo da wani bulo da ke gefen hanya. Ta yi tangal-tangal haka, kamar za ta faɗi.
“Shegiya! Wallahi kin sanya ni dariya a kan titi haka, kamar zautatta. Wai an gaji da ke, babu wanda ya gaji da ke. Su a ganin su, abin kunya ne ɗiyarsu ta kai kamar ki ba ta samu miji ba. Kuma suna tsoron abin kunya, musamman kada wani shege ya ɗirka maki ciki, ki haifar masu ɗan rariya.”
“Haba, haba, don Allah ki bar wannan maganar. Ai ni ban ga ɗa namijin da ya isa ya yi mani wannan sakarcin ba. Ki tuna fa ina da ilimi hagu da dama. Kin san dai na sauke Alƙur’ani bara, ga shi ma har na fara hadda. Arba’una Hadis kuwa tuni na sauke shi, har ma na fara shiga manyan littattafan Fiƙihu. Ta ɓangaren karatun zamani kuwa, ba sai na gaya maki ba, tun da aji ɗaya muke; kwalin difiloma kawai muke jira. Don haka, duk illar zinace-zinace ba wacce ba mu sani ba. To, yaushe zan zubar da mutuncina har in yarda da wani mayaudari ya yaudare ni?”
Zinatu na gama wannan batu sai Balaraba ta amshe, ta ce: “Ni dai ina ganin mu bi a hankali da iyayenmu, mu lallaɓa da su, mu rabu lafiya. Tun da dai mun yi karatun nan na zamani, sai mu ƙoƙarta mu yi ta roƙon Allah Ya koro mana da mazajen aure. Mu yi aurenmu mu huta, alabashi idan muna ɗakunan mazajenmu sai mu san hikimar da za mu shawo kansu, su bar mu mu ci gaba da neman ilimi ko kuma ma mu yi aiki ko sana’ar neman kuɗi, don rufin asirin kanmu.”
Da wannan zancen ne suka kawo inda za su rabu, kowace ta kama hanyar gidansu.
***
~~~~~~~
Za mu ci gaba a ranar Lahadi in sha Allahu. Ku ci gaba da bibiyar mu.
~~~~~~~













