• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, May 3, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

INEC Za Ta Gudanar Da Zaɓuɓɓukan Da Kotu Ta Soke Da Na Cike Gurabu 34 A Fabrairu 2024 – Yakubu

Daga Wakilinmu by Daga Wakilinmu
December 20, 2023
in Labarai
0
Zaɓen gwamna: Mutum 2,318,919 za su yi zaɓe a Imo, 1,833,160 a Kogi, 1,017,613 a Bayelsa, inji INEC

Shugaban Hukumar INEC, Farfesa Mahmud Yakubu

13
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

INEC za ta gudanar da zaɓuɓɓukan da kotu ta soke da na cike gurabu 34 cikin Fabrairu 2024 – Yakubu ko

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta bayyana cewa mai yiwuwa a satin farko na Fabrairu, 2024 za ta gudanar da ragowar zaɓuɓɓukan da za a sake da kuma na cike gurabun a wasu mazaɓu, yankuna da shiyyoyin tarayya da jihohi.

Related posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026

Shugaban hukumar, Farfasa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a taron da INEC ta yi da jam’iyyu ranar Litinin, a Abuja.

Yakubu ya ce INEC ta ɗaura aniyar gudanar da zaɓuɓɓukan biyu, wato zaɓukan da za a sake da kuma waɗanda ba a samu gudanarwa ba duk a rana ɗaya. Wato ya na nufin har da zaɓukan cike gurabu kenan.

Ya ƙara da cewa yayin da aka kafa Kotunan Sauraren Ƙararrakin Zaɓe bayan kammala zaɓen 2023, to yanzu dai za a ce sun kusa kammala zaman su.

“Abin da ya rage shi ne hukumar zaɓe ta gudanar da zaɓuɓɓukan da kotuna suka bada umarnin a sake a wuraren da za a sake zaɓuɓɓukan.

Yakubu ya ce INEC za ta kuma gudanar da zaɓuɓɓukan cike gurabun waɗanda suka mutu, ko waɗanda suka ajiye muƙaman da aka zaɓe su a kai a Majalisar Ƙasa ko Majalisar Jihohi.

“Kamar yadda ku ka sani, shi zaɓe na ‘re-run’, zaɓe ne da ya ƙunshi jam’iyyu da ‘yan takara waɗanda suka rigaya suka fafata a babban zaɓe. Sai fa idan jam’iyya na buƙatar musanya ɗan takara idan ya rasu kafin a sake wannan zaɓen da za a yi.

“Shi kuma ‘bye-election’, zaɓe ne sabo da za a yi. Don haka a wannan tsari, tilas ne jam’iyyu su sake gudanar da zaɓen fidda gwanaye cikin ƙa’idar kwanakin da dokar zaɓe ta gindaya.

“Zuwa yanzu dai Kotunan Ɗaukaka Ƙararrakin Zaɓe sun umarci INEC ta gudanar da zaɓuɓɓuka a mazaɓu 34 da suka ƙunshi shiyyar sanata ɗaya, sai mazaɓun ɗan majalisar tarayya guda 11 da majalisun jihohi 22.

“Sai dai kuma daga zaɓuɓɓuka 34 ɗin da za a sake, guda wurare uku ne kawai za a sake zaɓen baki ɗaya.”

A ƙarshe Yakubu ya ce sai bayan an kammala sauraren shari’un zaɓen gwamnoni a kotunan tarayya da Kotun Ƙoli, sannan hukumar sa za ta tattara yawan shari’un da aka gudanar, domin yin bayanin su dalla-dalla.

Previous Post

Gwamnatina Za Ta Mutunta ‘Yancin Kafafen Yaɗa Labarai

Next Post

Kafafen Yaɗa Labarai Su Ne Manyan Dirkokin Da Ke Ɗauke Da Nagartacciyar Dimokiraɗiyyarmu – Minista

Related Posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi
Labarai

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Labarai

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina
Labarai

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

February 13, 2026
Next Post
Kafafen Yaɗa Labarai Su Ne Manyan Dirkokin Da Ke Ɗauke Da Nagartacciyar Dimokiraɗiyyarmu – Minista

Kafafen Yaɗa Labarai Su Ne Manyan Dirkokin Da Ke Ɗauke Da Nagartacciyar Dimokiraɗiyyarmu - Minista

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Har Yanzu Akwai Cutar AIDS Kuma Za Mu Taru Mu Yaƙe Ta Da Gaske – Dokta Bala Nuhu

Har Yanzu Akwai Cutar AIDS Kuma Za Mu Taru Mu Yaƙe Ta Da Gaske – Dokta Bala Nuhu

July 6, 2023
DAGA TEBURIN RENO OMOKRI

DAGA TEBURIN RENO OMOKRI

March 21, 2025
Kar Nake Ganin Ka

Kar Nake Ganin Ka

May 29, 2023
WHEN THE SPIRIT WHISPERS: Littafin Tsarkake Tunani Da Samar Da Saita Rayuwa

WHEN THE SPIRIT WHISPERS: Littafin Tsarkake Tunani Da Samar Da Saita Rayuwa

October 11, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)
  • General Buratai (A Poem)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

April 28, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

April 27, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.