• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, January 22, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

HARIN JIRGIN SAMA GA MUSULMI: Ya Wajaba A Zurfafa Bincike Kuma A Biya Diyya

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
December 7, 2023
in Babban Labari
0
HARIN JIRGIN SAMA GA MUSULMI: Ya Wajaba A Zurfafa Bincike Kuma A Biya Diyya
14
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

HARIN JIRGIN SAMA GA MUSULMI: Ya Wajaba A Zurfafa Bincike Kuma A Biya Diyya

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

January 14, 2026
Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin

Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin

January 4, 2026

~~~~~~~
Abin da zai faru ƙaddararre ne daga Allah. Babu shakka ga wannan batu. Sai dai kuma abu ne mai kyau kuma mai tsari ga al’umma da su ɗauki darasi daga dukkan wani al’amari da ya faru da su, domin gyaran gaba.

Ina magana ne game da batun yadda wani jirgin Sojojin Najeriya ya jefa bamabamai ga wasu gungun mutane da suke bikin Mauludin Manzon Allah (saw), da maraicen Lahadi (3-12-2023) a ƙauyen Tudun Biri na Ƙaramar Hukumar Igabi, Jihar Kaduna, inda mutane sama da 80 suka rasa rayukansu, da dama kuma suka samu munanan raunuka.

A yau ba sai gobe ba, al’ummar Arewa, musamman Musulmi muna cikin jarabawa mai girma. An ƙulla mana ƙullalliya, an kitsa mana kitsatssa. An shirya mana yaƙin sunƙuru domin a wargaza mu. Lallai ne mu yi karatun-ta-natsu. Lallai ne mu hankalta, mu dawo cikin hayyacinmu, domin saita al’amuranmu zuwa hanya madaidaiciya.

A tsawon shekaru masu yawa da suka gabata, an ƙulla wa Arewa makirci da Boko Haram, wanda a sanadiyyar haka aka salwantar da rayuka marasa adadi. An tozarta iyalai da dama, an talauta wasu da dama, kamar yadda aka haddasa gaba da shakku da tsangwama tsakanin al’ummu.

An shigo mana da ‘yan bindiga daɗi, masu garkuwa mutane domin kuɗin fansa. A sanadiyyar haka, an ci zafafin mata, an tarwatsa iyalai, an maida wasu zawarawa, an maida yara marayu, an lalata tattalin arziƙin Arewa na noma da kiwo.

A makon jiya kuma sai ga wata bahallatsar da aka haddasa mana a Tudun Biri na Ƙaramar Hukumar Igabi, Jihar Kaduna.

Hukumomin Sojojin Najeriya sun ce wannan al’amari ya faru ne wai bisa “kuskure.” Kuskure kuwa? Lallai akwai tambayoyi da dama da ya kamata a yi, domin tantance wannan batu.

Shin waɗannan bayin Allah da aka jefa wa bam, ba bikin Mauludi suke gudanarwa ba? Shin hukumar ‘yan sanda da ta farin kaya ba su da masaniyar wannan biki?

Shin a yayin da jami’an da ke sarrafa jirgin nan suka ga dandazon mutane, ba su yi bincike mai zurfi ba? Shin sun tuntuɓi Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kaduna da Daraktan SSS domin neman ƙarin bayani ko kuwa kawai yanke hukunci suka yi?

Shin babu na’urar da za ta tantance abin da mutanen nan suke gudanarwa a cikin jirgin nan? Shin wane Kwamanda ne ya ba da umurnin saka waɗannan bamabamai a karo fiye da biyu? Kuma jefa bom shi ne mataki na ƙarshe da ya kamata a ce an ɗauka a daidai lokacin?

A daidai wannan lokaci da muke da Shugaban Ƙasa Musulmi, mataimakinsa Musulmi, Ministan Tsaro, babba da ƙarami duk Musulmi, lallai bai kamata a aikata wa al’ummar Arewa irin wannan ta’addanci da sunan kuskure ba.

Ya kamata shugabanninmu da mu kanmu mabiya mu gyara al’amuranmu. Mu daina yaudarar juna. Lallai ne hukumar ƙasa ta yi ƙwaƙƙwaran bincika domin hukunta duk mai hannu cikin wannan aika-aika. Kuma a yi hanzarin biyan diyya ga iyalan waɗanda suka rasu.

Lallai na yarda da Sha’iri mai fiƙira, Malam Sani Yusuf Ayagi, wanda ya tsara waɗannan baitoci:

Wata dai shari’ar sai Allah,
Ba dai mutum alƙali ba!

Shari’a ƙwarai ta lalace,
Ku biyo ni dangi kwai zance,
Zan bayyana ban ɓoye ba.

Ni na ji manya na cewa,
Shari’a ƙwarai gatan kowa,
Na yarda ba da musu nai ba.

Duk wanda an ka ci zalinshi,
Shari’a ka kai wa kukanshi,
Da a taimakar ba ƙarya ba.

Nan za a share hawayenshi,
Ta tsaya ta ƙwato haƙƙinshi,
Ba za ta yarda a danne ba.

A gurin shari’a kun gane,
Dukkan mutane kaf nata ne,
Ba ta nuna bambanci ɗaya ba.

Wani shugaba ko mai mulki,
Matsayinsa ko ya kai sarki,
Ba za ta duba muƙami ba.

Muna roƙon Allah (swt) Ya ji ƙan waɗanda suka rasa rayukansu a wannan hari. Waɗanda suka samu raunuka da asarar dukiya kuwa, Allah Ya ba su lafiya, Ya kuma mayar masu da mafi alheri.

~~~~~~~
Bashir Yahuza Malumfashi, Babban Editan Mujallar Taskar Gizago, marubuci kuma mai sharhi kan al’amuran yau da kullum.
Alhamis, 23-05-1445 (Hijriyya)
07-12-2023 (Miladiyya).
~~~~~~~

Previous Post

Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Wayar Da Kan Al’umma, Cusa Ɗa’a, Kishin Ƙasa Da Kyawawan Ɗabi’u

Next Post

Minista Ya Buƙaci Masu Sana’ar Talla A Kafafen Yaɗa Labarai Su Faɗakar Da Jama’a Game Da Shirye-Shiryen Tattalin Arziki Na Gwamnatin Tinubu

Related Posts

Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna
Babban Labari

Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

January 14, 2026
Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin
Babban Labari

Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin

January 4, 2026
Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci
Babban Labari

Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci

January 3, 2026
Next Post
Gargaɗin Amurka kan Nijeriya na tada hankulan jama’a, kuma ya na yin illa ga tattalin arzikin ƙasa – Minista

Minista Ya Buƙaci Masu Sana'ar Talla A Kafafen Yaɗa Labarai Su Faɗakar Da Jama'a Game Da Shirye-Shiryen Tattalin Arziki Na Gwamnatin Tinubu

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

THE PUNCH EDITORIAL ON BENUE: A FABRICATION IN SEARCH OF A SCAPEGOAT

THE PUNCH EDITORIAL ON BENUE: A FABRICATION IN SEARCH OF A SCAPEGOAT

June 18, 2025
A Review of Boko Haram and other Security Challenges in Nigeria

A Review of Boko Haram and other Security Challenges in Nigeria

April 20, 2024
GIZAGAWAN NAJERIYA Sun Yi Wa ‘Dan Uwansu Alkotonawi Gangamin Addu’a

GIZAGAWAN NAJERIYA Sun Yi Wa ‘Dan Uwansu Alkotonawi Gangamin Addu’a

May 29, 2023
JONATHAN – KWANKWASO: Sabon Lissafin 2027

JONATHAN – KWANKWASO: Sabon Lissafin 2027

August 15, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)
  • Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya
  • Nazari, Tsokaci Da Sharhin Littafin Tarkon Mut’a

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)

January 21, 2026
My 83rd Birthday and the Kindred Spirit

Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya

January 19, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.