HARIN JIRGIN SAMA GA MUSULMI: Ya Wajaba A Zurfafa Bincike Kuma A Biya Diyya
Daga Bashir Yahuza Malumfashi
~~~~~~~
Abin da zai faru ƙaddararre ne daga Allah. Babu shakka ga wannan batu. Sai dai kuma abu ne mai kyau kuma mai tsari ga al’umma da su ɗauki darasi daga dukkan wani al’amari da ya faru da su, domin gyaran gaba.
Ina magana ne game da batun yadda wani jirgin Sojojin Najeriya ya jefa bamabamai ga wasu gungun mutane da suke bikin Mauludin Manzon Allah (saw), da maraicen Lahadi (3-12-2023) a ƙauyen Tudun Biri na Ƙaramar Hukumar Igabi, Jihar Kaduna, inda mutane sama da 80 suka rasa rayukansu, da dama kuma suka samu munanan raunuka.
A yau ba sai gobe ba, al’ummar Arewa, musamman Musulmi muna cikin jarabawa mai girma. An ƙulla mana ƙullalliya, an kitsa mana kitsatssa. An shirya mana yaƙin sunƙuru domin a wargaza mu. Lallai ne mu yi karatun-ta-natsu. Lallai ne mu hankalta, mu dawo cikin hayyacinmu, domin saita al’amuranmu zuwa hanya madaidaiciya.
A tsawon shekaru masu yawa da suka gabata, an ƙulla wa Arewa makirci da Boko Haram, wanda a sanadiyyar haka aka salwantar da rayuka marasa adadi. An tozarta iyalai da dama, an talauta wasu da dama, kamar yadda aka haddasa gaba da shakku da tsangwama tsakanin al’ummu.
An shigo mana da ‘yan bindiga daɗi, masu garkuwa mutane domin kuɗin fansa. A sanadiyyar haka, an ci zafafin mata, an tarwatsa iyalai, an maida wasu zawarawa, an maida yara marayu, an lalata tattalin arziƙin Arewa na noma da kiwo.
A makon jiya kuma sai ga wata bahallatsar da aka haddasa mana a Tudun Biri na Ƙaramar Hukumar Igabi, Jihar Kaduna.
Hukumomin Sojojin Najeriya sun ce wannan al’amari ya faru ne wai bisa “kuskure.” Kuskure kuwa? Lallai akwai tambayoyi da dama da ya kamata a yi, domin tantance wannan batu.
Shin waɗannan bayin Allah da aka jefa wa bam, ba bikin Mauludi suke gudanarwa ba? Shin hukumar ‘yan sanda da ta farin kaya ba su da masaniyar wannan biki?
Shin a yayin da jami’an da ke sarrafa jirgin nan suka ga dandazon mutane, ba su yi bincike mai zurfi ba? Shin sun tuntuɓi Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kaduna da Daraktan SSS domin neman ƙarin bayani ko kuwa kawai yanke hukunci suka yi?
Shin babu na’urar da za ta tantance abin da mutanen nan suke gudanarwa a cikin jirgin nan? Shin wane Kwamanda ne ya ba da umurnin saka waɗannan bamabamai a karo fiye da biyu? Kuma jefa bom shi ne mataki na ƙarshe da ya kamata a ce an ɗauka a daidai lokacin?
A daidai wannan lokaci da muke da Shugaban Ƙasa Musulmi, mataimakinsa Musulmi, Ministan Tsaro, babba da ƙarami duk Musulmi, lallai bai kamata a aikata wa al’ummar Arewa irin wannan ta’addanci da sunan kuskure ba.
Ya kamata shugabanninmu da mu kanmu mabiya mu gyara al’amuranmu. Mu daina yaudarar juna. Lallai ne hukumar ƙasa ta yi ƙwaƙƙwaran bincika domin hukunta duk mai hannu cikin wannan aika-aika. Kuma a yi hanzarin biyan diyya ga iyalan waɗanda suka rasu.
Lallai na yarda da Sha’iri mai fiƙira, Malam Sani Yusuf Ayagi, wanda ya tsara waɗannan baitoci:
Wata dai shari’ar sai Allah,
Ba dai mutum alƙali ba!
Shari’a ƙwarai ta lalace,
Ku biyo ni dangi kwai zance,
Zan bayyana ban ɓoye ba.
Ni na ji manya na cewa,
Shari’a ƙwarai gatan kowa,
Na yarda ba da musu nai ba.
Duk wanda an ka ci zalinshi,
Shari’a ka kai wa kukanshi,
Da a taimakar ba ƙarya ba.
Nan za a share hawayenshi,
Ta tsaya ta ƙwato haƙƙinshi,
Ba za ta yarda a danne ba.
A gurin shari’a kun gane,
Dukkan mutane kaf nata ne,
Ba ta nuna bambanci ɗaya ba.
Wani shugaba ko mai mulki,
Matsayinsa ko ya kai sarki,
Ba za ta duba muƙami ba.
Muna roƙon Allah (swt) Ya ji ƙan waɗanda suka rasa rayukansu a wannan hari. Waɗanda suka samu raunuka da asarar dukiya kuwa, Allah Ya ba su lafiya, Ya kuma mayar masu da mafi alheri.
~~~~~~~
Bashir Yahuza Malumfashi, Babban Editan Mujallar Taskar Gizago, marubuci kuma mai sharhi kan al’amuran yau da kullum.
Alhamis, 23-05-1445 (Hijriyya)
07-12-2023 (Miladiyya).
~~~~~~~













