• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, April 24, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

HARIN JIRGIN SAMA GA MUSULMI: Ya Wajaba A Zurfafa Bincike Kuma A Biya Diyya

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
December 7, 2023
in Babban Labari
0
HARIN JIRGIN SAMA GA MUSULMI: Ya Wajaba A Zurfafa Bincike Kuma A Biya Diyya
15
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

HARIN JIRGIN SAMA GA MUSULMI: Ya Wajaba A Zurfafa Bincike Kuma A Biya Diyya

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

April 8, 2026

~~~~~~~
Abin da zai faru ƙaddararre ne daga Allah. Babu shakka ga wannan batu. Sai dai kuma abu ne mai kyau kuma mai tsari ga al’umma da su ɗauki darasi daga dukkan wani al’amari da ya faru da su, domin gyaran gaba.

Ina magana ne game da batun yadda wani jirgin Sojojin Najeriya ya jefa bamabamai ga wasu gungun mutane da suke bikin Mauludin Manzon Allah (saw), da maraicen Lahadi (3-12-2023) a ƙauyen Tudun Biri na Ƙaramar Hukumar Igabi, Jihar Kaduna, inda mutane sama da 80 suka rasa rayukansu, da dama kuma suka samu munanan raunuka.

A yau ba sai gobe ba, al’ummar Arewa, musamman Musulmi muna cikin jarabawa mai girma. An ƙulla mana ƙullalliya, an kitsa mana kitsatssa. An shirya mana yaƙin sunƙuru domin a wargaza mu. Lallai ne mu yi karatun-ta-natsu. Lallai ne mu hankalta, mu dawo cikin hayyacinmu, domin saita al’amuranmu zuwa hanya madaidaiciya.

A tsawon shekaru masu yawa da suka gabata, an ƙulla wa Arewa makirci da Boko Haram, wanda a sanadiyyar haka aka salwantar da rayuka marasa adadi. An tozarta iyalai da dama, an talauta wasu da dama, kamar yadda aka haddasa gaba da shakku da tsangwama tsakanin al’ummu.

An shigo mana da ‘yan bindiga daɗi, masu garkuwa mutane domin kuɗin fansa. A sanadiyyar haka, an ci zafafin mata, an tarwatsa iyalai, an maida wasu zawarawa, an maida yara marayu, an lalata tattalin arziƙin Arewa na noma da kiwo.

A makon jiya kuma sai ga wata bahallatsar da aka haddasa mana a Tudun Biri na Ƙaramar Hukumar Igabi, Jihar Kaduna.

Hukumomin Sojojin Najeriya sun ce wannan al’amari ya faru ne wai bisa “kuskure.” Kuskure kuwa? Lallai akwai tambayoyi da dama da ya kamata a yi, domin tantance wannan batu.

Shin waɗannan bayin Allah da aka jefa wa bam, ba bikin Mauludi suke gudanarwa ba? Shin hukumar ‘yan sanda da ta farin kaya ba su da masaniyar wannan biki?

Shin a yayin da jami’an da ke sarrafa jirgin nan suka ga dandazon mutane, ba su yi bincike mai zurfi ba? Shin sun tuntuɓi Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kaduna da Daraktan SSS domin neman ƙarin bayani ko kuwa kawai yanke hukunci suka yi?

Shin babu na’urar da za ta tantance abin da mutanen nan suke gudanarwa a cikin jirgin nan? Shin wane Kwamanda ne ya ba da umurnin saka waɗannan bamabamai a karo fiye da biyu? Kuma jefa bom shi ne mataki na ƙarshe da ya kamata a ce an ɗauka a daidai lokacin?

A daidai wannan lokaci da muke da Shugaban Ƙasa Musulmi, mataimakinsa Musulmi, Ministan Tsaro, babba da ƙarami duk Musulmi, lallai bai kamata a aikata wa al’ummar Arewa irin wannan ta’addanci da sunan kuskure ba.

Ya kamata shugabanninmu da mu kanmu mabiya mu gyara al’amuranmu. Mu daina yaudarar juna. Lallai ne hukumar ƙasa ta yi ƙwaƙƙwaran bincika domin hukunta duk mai hannu cikin wannan aika-aika. Kuma a yi hanzarin biyan diyya ga iyalan waɗanda suka rasu.

Lallai na yarda da Sha’iri mai fiƙira, Malam Sani Yusuf Ayagi, wanda ya tsara waɗannan baitoci:

Wata dai shari’ar sai Allah,
Ba dai mutum alƙali ba!

Shari’a ƙwarai ta lalace,
Ku biyo ni dangi kwai zance,
Zan bayyana ban ɓoye ba.

Ni na ji manya na cewa,
Shari’a ƙwarai gatan kowa,
Na yarda ba da musu nai ba.

Duk wanda an ka ci zalinshi,
Shari’a ka kai wa kukanshi,
Da a taimakar ba ƙarya ba.

Nan za a share hawayenshi,
Ta tsaya ta ƙwato haƙƙinshi,
Ba za ta yarda a danne ba.

A gurin shari’a kun gane,
Dukkan mutane kaf nata ne,
Ba ta nuna bambanci ɗaya ba.

Wani shugaba ko mai mulki,
Matsayinsa ko ya kai sarki,
Ba za ta duba muƙami ba.

Muna roƙon Allah (swt) Ya ji ƙan waɗanda suka rasa rayukansu a wannan hari. Waɗanda suka samu raunuka da asarar dukiya kuwa, Allah Ya ba su lafiya, Ya kuma mayar masu da mafi alheri.

~~~~~~~
Bashir Yahuza Malumfashi, Babban Editan Mujallar Taskar Gizago, marubuci kuma mai sharhi kan al’amuran yau da kullum.
Alhamis, 23-05-1445 (Hijriyya)
07-12-2023 (Miladiyya).
~~~~~~~

Previous Post

Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Wayar Da Kan Al’umma, Cusa Ɗa’a, Kishin Ƙasa Da Kyawawan Ɗabi’u

Next Post

Minista Ya Buƙaci Masu Sana’ar Talla A Kafafen Yaɗa Labarai Su Faɗakar Da Jama’a Game Da Shirye-Shiryen Tattalin Arziki Na Gwamnatin Tinubu

Related Posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Babban Labari

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume
Babban Labari

Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

April 8, 2026
Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel
Babban Labari

Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel

April 2, 2026
Next Post
Gargaɗin Amurka kan Nijeriya na tada hankulan jama’a, kuma ya na yin illa ga tattalin arzikin ƙasa – Minista

Minista Ya Buƙaci Masu Sana'ar Talla A Kafafen Yaɗa Labarai Su Faɗakar Da Jama'a Game Da Shirye-Shiryen Tattalin Arziki Na Gwamnatin Tinubu

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Dharmendra: Ta’aziyyar Bankwana Da Mashahurin Afto

Dharmendra: Ta’aziyyar Bankwana Da Mashahurin Afto

November 25, 2025
GENERAL BURATAI PAYS HOMAGE TO GENERAL BUHARI

GENERAL BURATAI PAYS HOMAGE TO GENERAL BUHARI

March 9, 2025
TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNKASA MALUMFASHI DA KEWAYE (8)

TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNKASA MALUMFASHI DA KEWAYE (8)

October 13, 2025
Wasu Mutane Sun Kitsa Tayar Da Hargitsi A Najeriya – DSS

Wasu Mutane Sun Kitsa Tayar Da Hargitsi A Najeriya – DSS

September 4, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Duniya Ba Gidan Zama Ba
  • Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi
  • Governor Dikko Radda Commissions Community Development Projects Built by Muntari Sagir in Malumfashi

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Duniya Ba Gidan Zama Ba

Duniya Ba Gidan Zama Ba

April 24, 2026
Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi

Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi

April 22, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.