FAƊA DA ‘YAN TA’ADDA: Malam Dikko Kada Ka Shiga Daji – Abdullahi Mahuta
~~~~~~~
An yi kira da nusarwa ga Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa da cewa ya canja tunani, kada ya yarda ya shiga daji domin faɗa da ‘yan ta’adda, kamar yadda ya ayyana a hirarsa da BBC Hausa.
Fitaccen ɗan siyasa a Jihar Katsina, Malam Abdullahi Ibrahim Mahuta ne ya bayar da wannan shawara ga gwamnan, a shafinsa na Facebook.
Kamar yadda ya ce, “ina wannan rubutu ne a dalilin wata hire da mai girma gwamna ya yi kwanan nan da gidan rediyo dio na BBC.
“A wannan hira, gwamna ya ƙara jaddada aniyarsa ta bin jami’an tsaro cikin daji domin a yaƙi waɗannan ‘yan ta’adda tare da shi.”
Mahuta, ya ci gaba da cewa, “duk wanda ya yi la’akari da matakan da Dokta Dikko Raɗɗa ya fara ɗauka domin kawo ƙarshen matsalar tsaro a Jihar Katsina zuwa yanzu, ba na tsammanin akwai mai sauran shakku na game da wannan niyya da sadaukarwa nasa.
“A bisa haka ne nake kira da kuma tunasar da gwamna cewa ɗaukar makami da shiga daji ba naka ba ne yallaɓai; ba na shugaba ba ne.
“Kamar yadda aka ruwaito sayyidina Abubakar ya taɓa faɗar cewa ‘abin da ke tafiyar da al’umma shi ne hikima ta dattawa da kuma ƙarfin jiki na matasa.’
“Abin da ke kanka a yanzu shi ne amfani da ilimi, hikima da basira da Allah Ya ba ka, domin samowa da kuma tsara hanyoyin da za a bi wajen magance wannan matsalar, kamar yadda ka fara yi a yanzu.”
Ɗan siyasar ya kuma ci gaba da kawo dalilan da ya sa yake nusar da Gwamnan, inda ya ce, “amma ainahin aiwatar da ko gudanar da yaƙin a daji, to wannan kuma na matasa ne da sauran jami’an tsaro, waɗanda ke da horo na musamman.
“Yallaɓai, idan da a ce cikin aikin soja kake, zuwa yanzu da kake da shekara 55, da yanzu kana kan muƙamin Janar. To su kuma Janarori ba su zuwa fagen daga, sukan yi tunga ne a tsakiya, suna shirya hikimomi da dabarun yadda za a fafata yaƙin a can filin daga.
“Ya mai girma Gwamna, mun fahimci irin himma da azamarka bisa ɗawainiya ga al’umma. Mu ma muna tare da kai a wannan himma amma don Allah kada a shiga dajin nan da kai.
“Mun san cewa alƙawari ne ka ɗauka lokacin kamfen, cewa za a shiga daji da kai. To ni dai na yafe wannan alƙawarin. Allah Ya kawo mana ƙarshen wannan matsalar a ƙasarmu.”
~~~~~~~













