• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, January 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

FAƊA DA ‘YAN TA’ADDA: Malam Dikko Kada Ka Shiga Daji – Abdullahi Mahuta

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
October 16, 2023
in Babban Labari
0
FAƊA DA ‘YAN TA’ADDA: Malam Dikko Kada Ka Shiga Daji – Abdullahi Mahuta

Gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa

36
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

FAƊA DA ‘YAN TA’ADDA: Malam Dikko Kada Ka Shiga Daji – Abdullahi Mahuta

~~~~~~~
An yi kira da nusarwa ga Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa da cewa ya canja tunani, kada ya yarda ya shiga daji domin faɗa da ‘yan ta’adda, kamar yadda ya ayyana a hirarsa da BBC Hausa.

Related posts

Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

January 14, 2026
Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin

Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin

January 4, 2026

Fitaccen ɗan siyasa a Jihar Katsina, Malam Abdullahi Ibrahim Mahuta ne ya bayar da wannan shawara ga gwamnan, a shafinsa na Facebook.

Kamar yadda ya ce, “ina wannan rubutu ne a dalilin wata hire da mai girma gwamna ya yi kwanan nan da gidan rediyo dio na BBC.

“A wannan hira, gwamna ya ƙara jaddada aniyarsa ta bin jami’an tsaro cikin daji domin a yaƙi waɗannan ‘yan ta’adda tare da shi.”

Mahuta, ya ci gaba da cewa, “duk wanda ya yi la’akari da matakan da Dokta Dikko Raɗɗa ya fara ɗauka domin kawo ƙarshen matsalar tsaro a Jihar Katsina zuwa yanzu, ba na tsammanin akwai mai sauran shakku na game da wannan niyya da sadaukarwa nasa.

“A bisa haka ne nake kira da kuma tunasar da gwamna cewa ɗaukar makami da shiga daji ba naka ba ne yallaɓai; ba na shugaba ba ne.

“Kamar yadda aka ruwaito sayyidina Abubakar ya taɓa faɗar cewa ‘abin da ke tafiyar da al’umma shi ne hikima ta dattawa da kuma ƙarfin jiki na matasa.’

“Abin da ke kanka a yanzu shi ne amfani da ilimi, hikima da basira da Allah Ya ba ka, domin samowa da kuma tsara hanyoyin da za a bi wajen magance wannan matsalar, kamar yadda ka fara yi a yanzu.”

Ɗan siyasar ya kuma ci gaba da kawo dalilan da ya sa yake nusar da Gwamnan, inda ya ce, “amma ainahin aiwatar da ko gudanar da yaƙin a daji, to wannan kuma na matasa ne da sauran jami’an tsaro, waɗanda ke da horo na musamman.

“Yallaɓai, idan da a ce cikin aikin soja kake, zuwa yanzu da kake da shekara 55, da yanzu kana kan muƙamin Janar. To su kuma Janarori ba su zuwa fagen daga, sukan yi tunga ne a tsakiya, suna shirya hikimomi da dabarun yadda za a fafata yaƙin a can filin daga.

“Ya mai girma Gwamna, mun fahimci irin himma da azamarka bisa ɗawainiya ga al’umma. Mu ma muna tare da kai a wannan himma amma don Allah kada a shiga dajin nan da kai.

“Mun san cewa alƙawari ne ka ɗauka lokacin kamfen, cewa za a shiga daji da kai. To ni dai na yafe wannan alƙawarin. Allah Ya kawo mana ƙarshen wannan matsalar a ƙasarmu.”
~~~~~~~

Previous Post

SATAR AZZAKARI: Gaskiya Ko Ruɗanin Tunani?

Next Post

Betaran Biu Janar Buratai Ya Samu Sarautar ‘Baakoren Akure’

Related Posts

Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna
Babban Labari

Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

January 14, 2026
Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin
Babban Labari

Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin

January 4, 2026
Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci
Babban Labari

Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci

January 3, 2026
Next Post
Betaran Biu Janar Buratai Ya Samu Sarautar ‘Baakoren Akure’

Betaran Biu Janar Buratai Ya Samu Sarautar 'Baakoren Akure'

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Kwamishina Saulawa Jajirtacce Ne – Dr. Bala Nuhu

Health: Daura sets to commission Federal Medical Center

September 9, 2023
SASSANYAN AMINCI (5)

SASSANYAN AMINCI (5)

September 12, 2025
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (6)

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (6)

January 6, 2026
ALIYU ƘANƘARA YA ZAMA FARFESA

ALIYU ƘANƘARA YA ZAMA FARFESA

October 7, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation
  • Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco
  • Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

January 15, 2026
Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.