• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Tuesday, May 19, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

Yan ta’addan Daji Kafirai Ne – Sarkin Musulmi

BABBAN LABARI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
May 8, 2026
in Babban Labari
0
Yan ta’addan Daji Kafirai Ne  – Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar III

9
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

‘Yan ta’addan Daji Kafirai Ne

– Sarkin Musulmi

Related posts

Ta Banka Wa Mijinta, Kishiyarta Da Yara Wuta A Kano

Ta Banka Wa Mijinta, Kishiyarta Da Yara Wuta A Kano

May 13, 2026
Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

May 9, 2026

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III

__________

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, ya bayyana cewa duk wanda yake kashe rayukan bayin Allah haka kawai, ba za a kira shi da Musulmi ba, duk kuwa da cewa yana faɗin “Allahu Akbar” a yayin da yake aikata ta’addancinsa.

Mai Alfarma ya jaddada cewa, makomar duk wani ɗan ta’adda, ita ce wuta, inda zai fuskanci azabar wannan mugun aiki da ya aikata. Ya ƙara da cewa yawancin tashe-tashen hankali da ake dangantawa da addini, ana fahimtarsu ne ba daidai ba, lamarin da ke ƙara haifar da zargi da rashin yarda tsakanin jama’a.

Kamar yadda Jaridar Vanguard ta ruwaito, Sultan Sa’ad ya bayyana hakan ne a Larabar da ta gabata, a yayin taron farko na bana, na Majalisar Addinai ta Ƙasa (NIREC) da aka gudanar a Abuja, a matsayinsa na shugaban majalisar. Sauran abokan aikinsa da suka yi jawabi a yayin taron, sun haɗa da Shugaban Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), Daniel Okoh da Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume.

Da yake fayyace matsayarsa dangane da ‘yan ta’adda, a cewarsa: “Mu gyara yadda ake bayyana wannan batu. Ta’addanci ba batun addini ba ne. Mu daina jawo addini cikin wannan al’amari.

“Ya kamata mu riƙa kiran su da sunansu na gaskiya na ‘yan ta’adda. A daina jingina laƙanin “Musulmi” gare su. A daina kiran su da masu laifi Musulmi, ko ‘yan ta’addan Musulmi, ko ‘yan bindigar Musulmi. Ko da mutum ya ce shi Musulmi ne, abin da yake aikatawa ya saɓa wa koyarwar Musulunci, to ba za a laƙa wa addini laifin da ya aikata ba.”

Yayin da yake danganta matsalar da jahilci, Sultan ya yi gargaɗi kan yadda wasu ke ƙaryar cewa sun mallaki ilimin addini, yana mai cewa: “Kasancewar mutum ya iya Larabci ba ya sa ya zama Sheikh. Larabci harshe ne kawai. Saboda haka ilimi yana da matuƙar muhimmanci.

“Wani zai iya zuwa kasuwa ya tayar da bam, ya kashe mutane sannan ya yi ihu da ‘Allahu Akbar.’ Eh, Allah Maɗaukaki ne amma kai za ka tafi zuwa wuta. Za ka sha azaba saboda kashe rayukan bayin Allah da kake yi, marasa laifi.” In ji Mai Alfarma Sarkin Musulmi.

A yayin taron na bana, an buƙaci mabiya addinai mabambanta a ƙasar nan da su kai zukatansu nesa, su samar da zaman lafiya da fahimtar juna. An jaddada cewa, kowane addini yana kira ne zuwa ga bautar Allah shi ɗaya, don haka bai dace a yi amfani da shi wajen haddasa fitina a tsakanin al’umma ba.

Previous Post

Farewell Ashaka

Next Post

Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

Related Posts

Ta Banka Wa Mijinta, Kishiyarta Da Yara Wuta A Kano
Babban Labari

Ta Banka Wa Mijinta, Kishiyarta Da Yara Wuta A Kano

May 13, 2026
Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi
Babban Labari

Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

May 9, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Babban Labari

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Next Post
Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

VENOM

VENOM

August 6, 2024
A Season of Locusts (Poetic Review)

A Season of Locusts (Poetic Review)

February 6, 2024
Sanadiyyar Rubutu, Zane Da Waƙa: Na Samu Arzikin Sanin Jama’a – Kamal

Sanadiyyar Rubutu, Zane Da Waƙa: Na Samu Arzikin Sanin Jama’a – Kamal

July 15, 2023
Malam Nasir El-Rufa’i: Guga Sha Kwaramniya

Wa Ke Tsoron Malam Elrufa’i Ya Zama Minista?

August 9, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Sule Lamido’s Theme of Authenticity
  • Turning Point Against Terror: The Fall of Abu-Bilal Al-Minuki
  • Barkanmu Da Shiga Watan Dhul-Hijjah 1447

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Sule Lamido’s Theme of Authenticity

Sule Lamido’s Theme of Authenticity

May 19, 2026
Turning Point Against Terror: The Fall of Abu-Bilal Al-Minuki

Turning Point Against Terror: The Fall of Abu-Bilal Al-Minuki

May 18, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.