Huɗubar Jumu’a A Taƙaice Daga Masallacin Unguwar Tumbu-Madallah
~~~~~~~
Wannan huɗubar an yi ta ne a ranar Juma’a, 01-02-1445 (Hijriyya)/18-08-2023 (Miladiyya), Limamin Masallacin Unguwar Tumbu da ke garin Madallah, Ƙaramar Hukumar Suleja, Jihar Neja; Liman ya buɗe huɗubarsa da godiya ga Allah Ubangijin talikai (swt), da salati da sallama ga Manzon Allah, Sallallahu alaihi Wasallam.
~~~~~~~
Maudu’in Huɗuba: Muhimmanci da wajibcin soyayyar juna tsakanin muminai.
Liman ya ce mu ji tsoron Allah, mu kyautata kuma mu ƙarfafa soyayyar juna da jaddada’yan uwantaka da zumunci. Ya ce muminai, musulmi ‘yan uwan juna ne da suka kasance kamar gini, wani sashe yana tallaba da ƙarfafa sashe.
Shin wai yaya soyayyar juna take? Liman ya ce idan za ka yi so, ka so don Allah da ManzonSa. Haka ma idan za ka nuna ƙi, to ka ƙi wanda ya ƙi Allah kuma ya ƙi Manzon Allah. Wannan ke nan yake nuna cewa Musulmi ya tabbatar da cewa, ya so ɗan uwansa Musulmi a duk lokacin da ya aikata aikin Allah. Haka kuma ya ƙi wanda ya ƙi Allah, wanda ke take dokokin Allah da ManzonSa.
Malam ya ce a ranar ƙiyama, za a rarrabe tsakanin Musulmi waɗanda suka so juna don Allah da waɗanda ba su yi haka ba. Waɗanda suka yi don Allah da ManzonSa ne kaɗai za su rabauta.
Babu wata alaƙa mai girma a gaban Allah da ManzonSa sai alaƙa da ‘yan uwantaka ta Musulunci. Kuma wajibi ne Musulmi ya yauƙaƙa dangantakarsa da ɗan uwansa ta hanyar taimakekeniyar juna.
Liman ya ce, a wannan zamani da ake cikin jarabawar rashin kuɗi da matsaloli iri-iri, shi ne lokacin da Musulmi ya kamata su taimaki juna. Mutum ya taimaki wanda bai da shi, mai ƙarfi ya tallafa wa mara ƙarfi. Wannan ne zai sanya so da ƙaunar juna a tsakanin Musulmi.
Liman ya yi sharhi kan wani hadisin Manzon Allah, wanda ke cewa, “Ba ya tare da mu, wanda ya ci ya ƙoshi alhali ɗan uwansa ya kwana da yunwa.” Wannan ke ƙara nuna mana cewa lallai ne mu taimaki juna, mu ƙarfafi juna, ta yadda marasa shi za su samu walwala a cikin al’umma.
Babu wata hanya da ke ƙarfafa soyayyar juna kamar taimakon juna. Musulmi su yawaita yin sallama tsakaninsu, domin sallama na kawo kusanci da soyayya kuma tana kai mutum zuwa aljanna. Kuma tana kawo yarda da haɗin kan al’umma. Tana magance gaba tsakanin al’umma. Don haka mu yawaita sallama, mu yawaita taimakon juna.
Liman ya ce Musulmi su kasance ‘yan uwan juna masu taushe fushi, masu yafiya ga juna, masu sakawa da kyakkyawa ga wanda ya aikata masu mummuna. Duk wanda ya kyautata wa ɗan uwansa, zai jawo ƙaunarsa kuma zai kusance shi. Hakan zai kawo zaman lafiya da haɗin kai kuma ya haifar da ƙarfi a cikin al’ummar musulmi.
Liman ya ce mu yi gaugawar ciyarwa ga ‘yan uwanmu marasa shi, mu taimaka wa addini, mu taimaka wa al’umma a lokacin tsanani da lokacin yalwa.
Ya ce Allah Yana son masu yafiya ga juna kuma Yana son masu kyautatawa.
Liman ya rufe huɗubarsa da addu’a, Allah Ya ƙarfafi al’ummar Musulmi, Ya wadata mu da ruwan sama mai albarka kuma Ya yaye mana wannan yanayi na ƙunci da rashin tsaro.
Amin summa Amin!
~~~~~~~













