SAKAMAKON ZAGAYE NA BIYU NA GASAR RUBUTU TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

_______________
Wannan gasa ta rubutun ƙirƙirarrun gajerun labarun Hausa, Zannan Galadiman Katsina, Walin Ƙafur, Cigarin Danejin Katsina, Manajan Darakta na Hukumar Ruwa ta Jihar Katsina, Injiniya Tukur Hassan Tingilin, FNSE ne ya ɗauki nauyin gabatar da ita, musamman domin ba da gudunmowa dangane da magance matsalolin tsaro, ilimantarwa, faɗakarwa da bunƙasa harshen Hausa.
Wadannan su ne sunayen labaru da marubutan da suka samu nasarar tsallake zagaye na biyu na wannan gasa.
Waɗannan marubuta 40, daga cikinsu ne za a zaɓi guda 20 mafiya inganci da gwanancewa a wannan gasa kuma da su ne za a gina littafi sukutum na wannan gasa. A zagaye na ƙarshe, daga cikin 20 ɗin ne kuma za a fitar da zakaru 3 mafiya gwanancewa.
Babu shakka marubutan nan sun nuna hazaƙa sosai. Muna roƙon Allah ya ba su nasara a zagaye na gaba. A ci gaba da sauraren sakamako na gaba, daga zaratan Alƙalanmu.
GA ZAKARU 40 DA SUKA YI NASARA:
1-SHUGABAN ƘASA – Binyaminu Zakari Hamisu.
2-MADUBI – Fadila Lamiɗo.
3-KU DUBE MU – Zainab Abdulrahman.
4-ALHAKI KWAIKWAYO – Ayuba Muhammad Ɗanzaki.
5-YANKAN BAYA – Hadiza Ibrahim Ɗan Auta.
6-HASKE DAGA DUHU – Isma’il Usman Abubakar.
7-WUTAR FANSA – Faisal Haruna Hunƙuyi.
8-MAFITARMU NA GARE MU – Mansura Sani Bashir.
9-YANKINA – Auwal Sumaiya.
10-TSUNTSAYEN DAJI – Mustapha Bashir.
11-FARMAKI – Ummulkhair Sani Panisau.
12-SITIYARIN MULKI – Na’ima Sulaiman Daƙayyawa.
13-TSUGUNE BA TA ƘARE BA – Aminu Ahmad Muhammad.
14-AREWA INA MUKA DOSA? – Mustapha Masoyin Baba.
15-MURYAR MARASA MURYA – Muttaƙa Ibrahim Nuhu Tafashiya.
16-ƊAN KUKA… – Hamida Sanusi Ahmad Fagge.
17-ƘARAR ƘAHO A ƘAUYE – Sani Muhammad Lawan.
18-LAIFI TUDU – Badamasi Hudu Tahir.
19-GOBENMU – Hassan Suleiman.
20-DA RUWAN CIKI… – Ruƙayya Adam Mu’az
21- YAƘI DA TSORO – Hafsat Ibrahim Khalil.
22-SAKAINAR KASHI – Fatima Umar.
23-RANA ZAFI – Lawan Muhammad Prp.
24-BAKIN ZARE – Jibrin Yusuf Kaila.
25-BAƘAR RANA – Fa’iza Abubakar.
26-MURYAR ZUCIYA – Hamza Dawaki.
27-MAKAUNIYAR AL’UMMA – Maimuna Iyami.
28-A DUBE MU – Maryam Ibrahim Liti.
29-KUKAN ZUCI – Rahinatou Mamoudou.
30-ƘASATA – Abubakar Sadik Abdullahi.
31-JARUMAR UWA – Lantana Ja’afar.
32-KUNYAR ƘARSHE – Hassana Labaran Ɗanlarabawa.
33-A HAIFI YARO DA ARZIƘI – Salmanu Faris Adamu.
34-MAFITAR GOBENMU – Zainab Mustafa Musa.
35-GARIN DA BA A BARCI – Fatima Abba Gana.
36-SADAUKARWA – Nafisa Ƙaura Goje.
37-RIBA BIYU – Khadijah Muhammad.
38-KU DUBE MU – Fatima Sunusi Rabi’u.
39-TSAKIYAR HAZO – Fauziyya Sani Jibril.
40-INUWAR ƘAYA – Abba Ubale Kibiya.
_______________













