GIRO ALLAH KYAUTA MAKWANCI
~~~~~~~
Allahu shi ya yi rayuwa.
Shi yai halittar mutuwa.
Rai idan dai yai faruwa,
Tabbata zai zo tuƙewa.
Giro Allah kyauta makwanci.
Mun shaidi kai malami ne,
Na Allah kai faƙihi ne,
Kai kira tsayye ko zaune,
A gyara don kar a ƙone,
Giro Allah kyauta makwanci.
Kai ne ka jaddada sunna.
Ka yi aiki babu sauna,
Ka yi yaƙin kau da ɓarna,
Ba ka girman kai da suna,
Giro Allah kyauta makwanci.
Kai kira gun mai sarauta,
Ko mai mulki kar sui cuta,
Ɗan kasuwa kar ya ɓata,
Attajirai su bar ƙaranta.
Giro Allah kyauta makwanci.
Kai gargaɗi gun su mata,
Su riƙe aurensu babu cuta,
Su mazan ma kar su keta,
Ƙa’idoji kada su manta.
Giro Allah kyauta makwanci.
Abubakar ka kwanta dama,
Jallah shi ya ba ka dama,
Ka bi hanyar hannun dama,
Ba ka inuwa da mai haɗama.
Giro Allah kyauta makwanci.
Ya Allah mun roƙe ka,
Yafe masa kai da kanka,
Hana shi shiga babbakakka,
Gyara bayansa da kanka.
Giro Allah kyauta makwanci.
~~~~~~~
© Bashir Yahuza Malumfashi,
Laraba 20-02-1445 (Hijiriyya)
06-09-2023 (Miladiyya)
~~~~~~~













Allah Ya gafarta masa da rahama Ya sanya Aljannah Firdaus ce makoma amin.