Nuhu Ribadu Ya Ɗau Hanyar Magance Satar Ɗanyen Mai
Daga Muhammadu Mustapha
A wani yunƙuri na ganin hukuma ta daƙile matsalar satar ɗanyen mai a Nigeria, a jiya Asabar ce Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara A Harkar Tsaro, Malam Nuhu Ribadu ya jagoranci wani ayari na musamman daga Fadar Shugaban Ƙasa, domin duba cibiyoyin man fetur da iskar gas a garin Owaza da ke Jithar Abia da kuma Odogwa na Karamar Hukumar Etche ta Jihar Ribas.
Kamar yadda jaridar Katsina Times ta ruwaito, Malam Nuhu Ribadu, ya ce har yanzu Nigeria na asarar ganga 400,000 na ɗanyen mai a kullum daga ɓarayin gida da na waje, duk da ƙoƙarin da gwamnati ke yi na kawo ƙarshen matsalar.
Ya ce ayyukan ɓarayin ɗanyen mai da masu fasa bututun man suna yin illa ga tattalin arzikin ƙasa, wanda kuma haka na daga cikin dalilan da ke haddasa tsadar rayuwa a ƙasar nan.
“Abin takaici ne cewa wasu mutane ƙalilan ne ke sace dukiyarmu, kuma a cikin haka za suke haifar da asara mai muni ga ƙasa ga jama’a.
“Nigeria na da ƙarfin samar da gangar ɗanyen mai miliyan 2 a kullum, amma a halin yanzu muna samar da ƙasa da ganga miliyan 1.6 saboda matsalar masu sata da lalata bututun mai.” In ji Malam Ribadu.
Da yake ƙimanta yawan ɓarnar da ɓarayin ke yi, ya ce: “Muna magana game da ganga 400,000 na ɗanyen mai da ake ɓarnatarwa, da wasu masu aikata laifi da yi wa ƙasa zagon-ƙasa da tattalin arziki ke aikatawa. Dalili ke nan ya sa ba ma samun riba mai yawa.”













Allah Ya taimaka
Amin Amin. Mun gode, Malam.