Shugabanci A Aikace: Gwamna Raɗɗa Ya Jagoranci Jami’an Tsaro Wajen Farautar ‘Yan Ta’adda


Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa ya jagoranci jami’an hukumomin tsaro na jihar zuwa farautar ƙasurguman masu aikata laifi, musamman ‘yan ta’adda a maɓuyarsu a ƙaaryar birnin Katsina.
A wata takardar manema labarai da Babban Sakataren Watsa Labarai na Gwamna, Ibrahim Kaula Mohammed ya rarraba, ya ce Gwamna Raɗɗa da kansa ya shiga gaba, ya jagoranci jami’an tsaron, inda suka farmaki maɓuyar ‘yan ta’addar da daren Talatar da ta gabata.
“Tun misalin ƙarfe 10 na dare suka fita aikin, har zuwa ƙarfe 11:30,” in ji Kaula.
Kamar yadda bayanan suka gabata, Gwamna da ayarin jami’an tsaron sun shiga unguwannin Sabuwar Unguwa, Sharara Pipe, Ɗanhaƙo, Filin Polo, Ƙofar Guga da kuma Tudun Matawalle.
“Yan ta’addan sun addabi mazauna unguwannin da ma sauran sassan birnin. Cikinsu akwai ɓarayin da suka ƙware a ƙwacen waya da amshe dukiya.” Kamar yadda Kaula Mohammed ya bayyana.
A ƙoƙarinsa na ganin ya kakkaɓe muggan masu aikata laifuka a jihar, Gwamna Raɗɗa ya umurci jami’an tsaro a jihar da su tashi tsaye, su yi aiki wurjanjan domin kakkaɓe duk wani ɗan ta’adda daga jihar.
Haka kuma a safiyar yau Laraba, Gwamnan ya kira taron gaggawa na shugabannin hukumomin tsaro da ke jihar, inda aka tattauna yadda za a magance matsalar tsaro da ta dawo a wasu sassa na jihar.
Ya nuna takaicinsa dangane da ƙalubalen rashin tsaro da ke addabar jihar. Don haka ya buƙaci shugabannin hukumomin tsaron da su ƙara ƙaimi a aikinsu, kamar yadda dokar ƙasa ta tanadar.













