Gwamnan Katsina Ya Taya Murna Ga Ganduje Da Sauran Shugabannin APC
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa ya aika da saƙon taya murna ga tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dokta Abdullahi Umar Ganduje bisa naɗinsa muƙamin Shugaban Jam’iyyar APC da kuma Sanata Ajibola Basiru, da aka naɗa a muƙamin Sakataren Jam’iyyar na ƙasa.
Tun da farko dai, an zaɓi Ganduje da Basiru ne a hukumance, a matsayin Shugaban Jam’iyya na Ƙasa da kuma Sakataren Jam’iyyar APC na Ƙasa a yayin taron Babban Kwamitin Jam’iyyar APC na Ƙasa Karo na 12, wanda ya gudanar a ranar Alhamis da ta gabata.
Ganduje, wanda bai jima da kammala mulkin Jihar Kano ba na tsawon shekara takwas, ya gaji Sanata Abdullahi Adamu, tsohon Gwamnan Jihar Nasarawa, a shugabancin jam’iyyar ta APC.
“Gwamna Dikko Raɗɗa ya bayyana goyon bayansa ga Ganduje, wanda yake da cancanta da ƙwarewar da zai shugabanci Jam’iyyar APC zuwa ga nasara.
“Ya bayyana cewa Ganduje ƙwararren ɗan siyasa ne, wanda zai iya amfani da gogewarsa wajen ba da gudunmawa wajen ɗaga martabar jam’iyyar zuwa ga nasara,” kamar yadda Ibrahim Kaula Mohammed, Babban Sakataren Watsa Labarai na Gwamna Raɗɗa ya bayyana a takardar manema labarai da ya fitar.
A ta bakin Gwamna Raɗɗa, “Ina taya murna ga sababbin zaɓaɓɓun shugabannin jam’iyyarmu na ƙasa. Zaɓensu a wannan muhimmin lokaci na siyasar ƙasa, abu ne mai dacewa kuma ba ni da tababa bisa cancanta da gogewarsu. Lallai za su yi nasarar kai jam’iyyarmu zuwa ga tudun tsira.”
Haka kuma, Gwamna Dikko Raɗɗa, wanda shi ne Sakataren Walwala na Ƙasa na farko na Jam’iyyar APC, ya jaddada amanna da cewa shugabancin Ganduje da Basiru zai haifar da nasarar da ake bukata ta bunkasa Najeriya ta fuskar tattalin arziki da inganta ƙasa, a shugabancin Shugaba Bola Ahmad Tinubu.













