Ibtila’in Ambaliya Ya Cinye Mace Da Goyonta A Zariya
Daga Wakilinmu

______________
Aƙalla mutane biyu ne suka rasa rayukansu, a yayin da wasu biyun suka ɓace sakamakon ambaliya a garin Zariya, Jihar Kaduna, a ranar Litinin da ta gabata.
Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, lamarin ya faru ne a Unguwar Tudun Jukun, bayan saukar wani mamakon ruwan sama. An an gano gawar wata yarinya ’yar shekara 18, Fatima Sani Dan Marke, wacce ɗaliba ce a makarantar School of Basic and Remedial Studies, Funtua, da kuma wani ɗalibi, Yusuf Surajo da ake kira Abba, a gadar makarantar firamare ta Isan Nabawa a Tudun Wada, Zariya.

An gano gawar Surajo a ranar Litinin, sai dai ita Fatima, an samo tata a washegari Talata. Amma ƙanwar Fatima mai shekara uku, Haneefa, har yanzu ba a ganta ba. An yi jana’izarta da misalin ƙarfe 4:00 na yamma a juya Talata, a Tudun Jukun, Zariya.
Fatima ɗiyar Alhaji Sani Danmarke ce, wanda aka fi sani da ASD, babban ɗan kasuwa a harkar taki a PZ, Sabongari, Zariya. A lokacin faruwar lamarin, tana goye da ƙanwarta Haneefa mai shekara uku a bayanta. Sun fito ne daga gidan kakarsu da ke Magume zuwa gidansu a Tudun Jukun, inda tazarar ba ta da nisa sosai, ko a ƙafa za a iya takawa. Amma abin tsausayi, sai malaminsu na Islamiyya, Malam Daddy ya ɗauke su a kan babur ɗinsa da sunan rage hanya.

Shaidun gani da ido sun ce ibtila’in ya auku ne a kusa da wani coci mai suna Nasara Baptist Church da ke kan titin Gaskiya a Tudun Jukun. Sun ce yayin da Malam Daddy ya tsira, ita Fatima da ƙanwarta Haneefa, ruwan ya tafi da su.
Wani shaidar gani da ido, Mustapha Badamasi Ɗanbakano, ya ce Fatima da ƙanwarta sun sauka daga babur ɗin ne a lokacin da babur ɗin malamin nasu ya bugi gaɓar kwalbati.
“Yarinyar ta yi saurin sauka daga babur, amma yayin da take ƙoƙarin ƙetare gabar kwalbatin sai ƙafarta ta zame ta faɗa cikin ruwa, tare da ƙanwarta da take goye a bayanta. Nan take ruwa ya kwashe su,” in ji shi. Ya ƙara da cewa wani mutum da ke tsaye a wajen, ya faɗa cikin ruwan da nufin don ceto su, shi ma kuma ya tafi da shi.

“Mutumin mazaunin Gidan Ɗangoma ne a Tudun Jukun, Zariya, kuma an yi masa jana’iza da safiyar yau bisa ga tsarin Musulunci,” in ji shi.
Malam Musa Umar Al-Mishawi, limamin da ya jagoranci jana’izar Yusuf Surajo a Kwarin Ɗangoma, Tudun Jukun, Zariya, ya tabbatar da cewa matashin ya samu rauni a goshinsa bayan ya bugi wani rodi da ke cikin ruwan.
Wurin da ibtila’in ya faru, a Unguwar Tudun Jukun ta Zariya, mahaɗar hanyar ruwa ce da ta taso daga Tukur Tukur zuwa Tudun Jukun, da kuma daga Magume zuwa Kwarin Ɗangoma, duk suna kusa da kogin Kubanni da aka sani tun da daɗewa yana cin rayuka. Sai dai wasu mazauna unguwar sun danganta wannan lamari na baya-bayan nan da ruwan sama mai tsanani yake mamaye magudanan ruwan.
Sun bayyana cewa daga Barewa Junction zuwa Gaskiya Corporation, an rufe magudanar amma daga can zuwa gadar kogin Kamacha, an bar ta buɗe. A wannan wurin ne aka samu wannan ibtila’i, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
A cewar mazauna wurin, da a ce an rufe wannan ɓangare ma, da wataƙila an kauce wa ambaliyar kuma da lamarin bai faru ba. Sun yi kira ga hukumomi da su ɗauki matakin da ya dace, na kawo gyara domin dakatar da faruwar haka a gaba.













