• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, March 8, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Shanshani

KAMUN LUDAYIN JEMAGE

Mukhtar Mudi Sipikin by Mukhtar Mudi Sipikin
August 5, 2023
in Shanshani
2
KAMUN LUDAYIN JEMAGE

Kamun Ludayin Jemage

69
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

KAMUN LUDAYIN JEMAGE

Daga Mukhtar Mudi Sipikin

Related posts

SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU

SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU

December 22, 2023
KAMUN LUDAYIN JEMAGE

KAMUN LUDAYIN JEMAGE (26-08-2023 da 02-09-2023)

September 2, 2023

Hazbiya ta kalli dandazon Tsuntsayen, ta ce: “Wannan satin fa an sha kwaramniya a dajin nan da kuma maƙwbtansa. Lamarin ma har sai Tsuntsu ya rasa gane wane abu ne ya fi jan hankali?”

Salwa ta ce: “Ni abin da ya ban mamaki shi ne, labarin da na ji a kan tsuntsayen Jihar Kyawawa, da yunwa ta ishe su, har ta kai sun cire tsoro sun fasa rumban tsaki. Gaskiya lamarin da ban tausayi. Tsuntsaye tura ta fara kai su bango fa, lallai Jemage ya kamata ya yi abin da ya dace, don a samu sauƙi.”

Kurciya ta yi murmushin ƙarfin hali, sannan ta kada baki ta ce: “Da alama ba ki saurari hirarsa da masu rahoto ba, ai ya bayyana cewa wai hanyar nan ita kaɗai ce tilo, da za ta kai mu tudun mun tsira!

“Wani abin haushin ma da takaici da rainin hankali, shi ne, wai ya san irin wahalar da mu ke sha, ku ji fa? Jemagen da sama da shekara arba’in bai san wahalar tsaki ba, kullum tsaki yake samu mai taushi ga ruwan sukar yana korawa yana jiƙa maƙoshinsa, yana daga cikin sheƙarsa ba tare da ya fita kiwo ba, wai shi zai kalle mu ya ce “Wai ya san irin wahalar da mu ke sha!” Kullum yana cikin ‘latu da daula, yana tashi cikin ayarin masu gadi, ‘yayansa suna fantamawa sannan…” Kurciya ta fashe da kuka.

Gado da ke gefenta, cikin rarrashi ya ce: “Ki yi haƙuri, tabbas abun na su da rainin hankali. Ni abin da yake ƙara ɓata min rai ma shi ne, tun zamanin Babba-Da-Jaka ake cewa wai za a buɗe rumbu a raba wa tsuntsaye tsaki amma har yau shiru. Ga shi shi ma Jemage ya ɗora da wannan maganar mai kama da tatsuniya, har yau ba tsuntsun da zai tabbatar maka da cewa ya amfana da tsakin da ake cewa an raba!”

Bainu ta ce: “Ni kuma abin da ke ƙara ba ni haushi, shi ne, yadda aka mayar da mu mabarata mayunwata! Wai za a raba mana tsaki kyauta! A faɗa wa Jemage ya riƙe tsakinsa, mu abin da muke so a sassauta mana, mu dinga siye da sulallanmu da arha, mu ba cima zaune ba ne, ba kamar shi da ake ciyar da shi da kuɗinmu ba!”

Tantabara, wadda tun da aka fara hirar ba ta ce komai ba, ta ce: “Ni fa na lura kamar ba ku damu da rigimar da Jemage ke san cilla mu ciki ba ko? Ko ba ku da labarin Jemage ya dage sai ya dawo da hamɓararren Shugaban tsuntsuyen maƙwabtanmu ne?
Wannan abu ba ƙaramar matsala zai cilla Arewancin dajin nan namu ba, lallai ne tsofaffinmu da ‘yan shila, da kowa da kowa ya fito ya yi Allah wadai da wannan aniyar ta Jemage da abokansa.”

Alhudahuda ya ce: “Ƙwarai kuwa, The prospective deployment of Mikiya force by Jemage and co, to countermand “Maƙwbtan Dajinmu” post-coup situation may herald a perilous concatenation of escalating hostilities, imperiling the lives and welfare of hapless civilians. Rather than this precipitate bellicosity, prioritizing the diplomatic entreaty, conciliatory mediation, and political dialogue would proffer a sagacious recourse towards ameliorating the crisis and galvanizing democratic governance and equilibrium…”

“Dakata! Alhudahuda, yanzu fa ba lokacin dogon Turanci ba ne, lokacin aiki ne. Dole ne mu yi wani abu kan wannan matsalar, in Jemage ya yi mana nisa dole mu tilasta wa Majalisar Ragon-Maza da ke wakiltar mu, da zu taka wa Jemage birki!”
Hazbiya ta katse shi.

Kanari ta ce: “Ba don dare ya yi ba, da mun tattauna matsalar ‘yar uwarmu da aka ba ta muƙami aka ƙwace…”

“Ma tattauna wani satin, Allah Ya tashe mu lafiya.” Hazbiya ta katse Kanari. Tsuntsaye suka yi sallama, kowa ya nufi sheƙarsa.

*An hango Ungulu da muƙarrabanta suna ta murnar kasancewar shugaban tsuntsaye masu riƙon Tsintsiyar Daji. Sannan an jiyo su, suna faɗar baƙaƙen maganganu ga Shugaban Rundunar Tsuntsaye Jan-Baki.

~~~~~~~
Malam Mukhtar marubuci, ɗan kasuwa kuma ɗan siyasa ne a Jihar Kano (05-08-2023)
~~~~~~~

Previous Post

Ba Mu Goyon Bayan Juyin Mulki Kuma Ba Ma Goyon Bayan Yaƙi Da Niger

Next Post

Gwamnan Katsina Ya Taya Murna Ga Ganduje Da Sauran Shugabannin APC

Related Posts

SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU
Shanshani

SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU

December 22, 2023
KAMUN LUDAYIN JEMAGE
Shanshani

KAMUN LUDAYIN JEMAGE (26-08-2023 da 02-09-2023)

September 2, 2023
KAMUN LUDAYIN JEMAGE
Shanshani

KAMUN LADUYIN JEMAGE (19-08-2023)

August 20, 2023
Next Post
Gwamnan Katsina Ya Taya Murna Ga Ganduje Da Sauran Shugabannin APC

Gwamnan Katsina Ya Taya Murna Ga Ganduje Da Sauran Shugabannin APC

Comments 2

  1. K. Bello Kiyawa says:
    3 years ago

    Ma sha Allahu, Allah ƙara basira Ya kuma kawo mana ɗauki cikin wannan halin da muke

    Reply
    • Bashir Yahuza Malumfashi says:
      3 years ago

      Amin Amin Ya Allah. Muna godiya da jimirinku na bibiyar jaridar nan. Muna maraba da shawarwari daga gare ku, yadda za mu inganta ayyukanmu, domin gamsarwa gare ku. Mun gode sosai.

      Reply

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Intelligence and Collaboration: Key to Defeating Insurgency in Nigeria – General Buratai

Intelligence and Collaboration: Key to Defeating Insurgency in Nigeria – General Buratai

March 5, 2025
SUBHANALLAHI: ‘Yan Sanda Sun Kulle Danladi Haruna

SUBHANALLAHI: ‘Yan Sanda Sun Kulle Danladi Haruna

October 7, 2023
ACF to TINUBU: MR. PRESIDENT, YOUR GOVERNMENT NEGLECTS AND SIDELINES AREWA

ACF to TINUBU: MR. PRESIDENT, YOUR GOVERNMENT NEGLECTS AND SIDELINES AREWA

August 1, 2025
TSOKACINMU NA YAU (18)

TSOKACINMU NA YAU (18)

March 18, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • RAMADAN KARIM: 19-1447
  • FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)
  • RAMADAN KARIM: 18-1447

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

RAMADAN KARIM: 19-1447

RAMADAN KARIM: 19-1447

March 8, 2026
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.