Ba Mu Goyon Bayan Juyin Mulki Kuma Ba Ma Goyon Bayan Yaƙi Da Niger
Daga Sharif Medoki
Shi Fa Tinubu bai San Alak’ar ‘yan Arewacin Nigeria Da Niger Ba
Gaskiyar magana ban goyi bayan juyin mulkin da aka yi a Niger ba amma kuma ba na goyon bayan ECOWAS ta kai hari Jamhuriyar Niger.
Jihohi bakwai na Arewacin Nigeria suna da iyaka da Niger, haka kuma sauran jihohin Arewa Maso Gabas, da Arewa Maso Yamma, watau dai Jihohi 13 da wasu Jihohi 3 na Arewa ta Tsakiya. Haka kuma mafi yawan al’umarsu suna da alaƙa da Niger.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ɗan yankin Kudu Maso Yamma ne. Ba lallai ba ne ya san alaƙar Arewacin Nigeria da Niger ba. Zai yiwu shi ya sa ya aminta da shawarar ECOWAS, a kan a kai hari Jamhuriyar Niger.
Kada fa ‘yan Arewa su manta, zai yiwu ‘yan Kudancin Nigeria su sanya siyasa a kan ɗaukar matakin Soja a Niger. Anya kuwa ɗaukar wancan matakin zai haifar wa da Nigeria ɗa mai ido?
Idan kuma Shugaba Tinubu ya san Aalaƙar, me ya sa ya tura Janar Abdussalm da Ambasada Kingibe zuwa Niger? Ina zaton don ya san nasabarsu ta shafi Jamhuriyar Niger ne.
Ba don kada a ce na yi tone-tone ba, da na lissafto muku sunayen sanannun ‘yan Nigeria masu mulki da a attajirai, waɗanda suke da jinin Jamhuriyar Niger.
Ya Ilahi, mene ne ribarmu, idan mun goyi bayan a kai wa ‘yan Jamhuriyar Niger hari?












