Gwamnan Jihar Jigawa Alhaji Umar Namadi ya ce sun gama tanadin taimakawa monama a jihar domin rage musu raɗaɗin cire tallafin man fetur da aka yi.
Cikin wata tattaunawa ta musamman da ya yi da BBC, Gwamna Namadi ya ce matakin farko da suka ɗauka shi ne rage farashin takin zamani daga Naira dubu, 26 zuwa Naira dubu 16.
Gwamnan ya ce suna sane da irin ƙalubalen da cire tallafin mai ya haifar wanda hakan ya jefa mutane cikin matsi, amma suna da fatan hakan zai zamar wa mutanen Najeriya alheri a gaba.
Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da Gwamnatin Tarayya ta sanar da shiri fara raba hatsi a faɗin Najeriya, domin rage wa al’ummarta zafin halin da cire tallafin ya jefa su.
“Kowacce jiha ta tsara abubuwa da yawa da za a yi, yanzu misali mu Jihar Jigawa, jiha ce ta manoma don haka tanadinmu na taimaka wa manoma ne.
“Za mu samar musu da abubuwa cikin sauƙi domin su samu su yi noma cikin sauƙi, abinci ya wadata, domin samun abinci wadatacce shi ne zai rage halin da ake ciki a yanzu.
“Na farko dai mun karya farashin taƙi daga Naira 26,000 zuwa Naira 16,000, kuma mun ɗauki matakai masu tsauri kan cewa sai manomi na ƙasa ne aka amince a sayarwa da takin,” in ji Gwamna Alhaji Umar Namadi.













