Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Huɗubar Jumu’a Daga Limamin Masallacin Unguwar Tumbu – Madallah
A yau Juma’a, 26-12-1444 (Hijriyya), 14-07-2023 (Miladiyya), a Masallacin Unguwar Tumbu da ke Garin Madallah, Ƙaramar Hukumar Tafa, Jihar Neja; Liman ya buɗe huɗubarsa da godiya ga Allah da yabo da salati ga fiyayyen talikai, Manzon Allah (saw). Sannan ya fara gabatar da huɗubar mai taken: “Mu Guji Zalunci, Mu Ji Tsoron Allah.”
Malam ya bayyana cewa lallai zalunci abin ƙi ne, saɓon Allah ne kuma alfasha ne, wanda duhu ne a ranar ƙiyama. Ya gargaɗe mu da mu kauce wa zalunci kowane iri, domin sakamakonsa azaba mai raɗaɗi ga wanda ya tafi lahira da haƙƙin zaluntar wani.
Malam ya gabatar da wani hadisi, wanda ke nuna yanayin ranar tashin ƙiyama a matsayin ranar tashin hankali, ranar da komai zai zama zafi da uƙuba. Sai dai a ranar akwai rukunin mutane bakwai da za su tsira, waɗanda za su shiga “Inuwar Allah” ta musamman. Waɗannan kuwa su ne:
1-Adalin shugaba wanda ya guje wa zaluntar waɗanda yake wa jagora. 2-Mutum mai bautar Allah da gaskiya, wanda bai shagaltar da rayuwarsa ga aikin assha ba, sai dai bautar Allah. 3-Matashi da ya rataya rayuwarsa ga masallaci, shi ne hidima da ibada da raya shi. 4-Mutane biyu da suka haɗu cikin zumunci da soyayya don Allah kawai. 5-Mutumin da ya guje wa riya, mai yin sadaka da hannun dama, alhali hagunsa bai san abin da ya bayar ba. 6-Mutumin da wata mace mai ɗaukaka da dukiya ta neme shi da alfasha, amma ya ƙiya saboda tsoron Allah. 7-Mutumin da ya kaɗaice cikin tunanin tsoron Allah har hawaye ya zubo masa.
Liman ya ci gaba da huɗuba, inda ya bayyana cewa zalunci iri uku ne, kamar haka:
1-Shirka, watau tara bautar Allah da wanin Allah (babban zalunci) ne. 2-Mutum ya zalunci wani mutum ko halitta a dukiyarsa ko jikinsa, da sauransu. 3-Mutum ya zalunci kansa da kansa, ta hanyar dulmiya cikin aikata saɓon Allah.
Malam ya gargaɗi mutane da su tuba daga aikata zalunci, su biya haƙƙin waɗanda suka zalunta tun a duniya, kafin a je lahira, inda babu abin biya, sai dai a ɗebi aikin ladar mutum a biya, ko kuma a ɗebi zunubin wanda aka zalunta a lafta wa mai zaluncin, idan bai da aikin ƙwarai.
Malam dai ya ja hankalin mutane da cewa lallai akwai hisabi ranar lahira, don haka mu ƙaurace wa zalunci.
Liman ya rufe huɗubarsa da addu’a ga al’umma da fatan mu gama da duniya lafiya. Haka kuma ya yi salati da sallama ga Manzon Allah, Annabi Muhammadu (saw).
Allah sa mu dace, Ya amintar da mu duniya da lahira, amin.












