TSOKACINMU NA YAU (06)
Yau Alhamis, 06-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 06-Maris-2025, Miladiyya.
Ga tsokacinmu na yau:
“Ya ku ‘yan uwa, yau za mu tattauna ne game da muhimmancin LOKACI. Mene ne lokaci? Shi ne wa’adin da ke zagaye da tafiyar rayuwarmu. Tun daga daƙiƙa zuwa minti zuwa awa zuwa yini zuwa mako zuwa wata, har zuwa shekara. Kowane adadin wa’adi, muhimmi ne ga rayuwarmu.
Kowace daƙiƙa ta zo ta wuce, shi ke nan ta wuce, har abada ba za ta sake dawowa ba. Dalili ke nan masu iya magana suke cewa, lokaci ba ya jiran kowa.
Wannan shi yake ƙara tabbatar mana da cewa, zaɓi yana wajenmu – ko dai mu yi aikin alheri a cikin lokacinmu ko akasin haka. Domin mu ci gajiyar lokacinmu, mu tsara shi daki-daki domin aiwatar da al’amuranmu masu muhimmanci a cikinsa. Mu kiyayi ɓata lokacinmu wajen yin abubuwan banza.”
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.











