Daga Yusuf Dingyaɗi
Zamantakewa: Kowace Mace Na Buƙatar Namiji Kusa Da Ita
Tun daga lokacin da ake ta ribbibin rubuce-rubuce a kan zancen wanki da mace za ta yi wa miji, nake tunani tare da neman gano, shin me ya kawo wannan ne?
Irin mu da Allah Ya yi wa rufin asiri na kasancewa da mata biyu fiye da shekaru 20 zuwa yau, sai mutum ya kalli meye zancen wanki a cikin hulɗa ta aure?
Na fi ganin wannan ga talauci, ƙurciya da rashin tunani a kan masu yaɗa wannan, don kuwa ƙima, ɗaukaka da daraja na auratayya sun fi ƙarfin zancen yi wa miji wanki.
Wani lokaci sai na yi rubutu in goge, mussaman dangane da matan da ke ganin kansu ‘Indepedent’ daga ikon mazaje saboda tsabar wayewa ko rayuwa ta zamani.
Hakan ya sanya na ɗan saurara, sai yanzu ma ake gaya mani cewa wasu da ke ta yaɗa wannan shaiɗancin, tun haihuwa har lokacin girmansu iyaye mazaje ke ɗauke da nauyinsu, tun daga abinci, sutura, motar hawa har gidan da suke barci; sakamakon mazajen aure sun yi kamfa saboda ganin halayarsu, da ganin irin rayuwar da suke ciki ta wayewa.
Sai dai, na tabbata akwai irin Malala a cikinsu, waɗanda idan suka yi wuf da NAMIJI, tabbata ba su sake SURUTU.
Fahimtarsu a kan Namiji ta game kowa, saboda sun samu matsala da namiji ɗaya ko biyu a aure ko hulɗa, dalilinsu kevnan a kan ɗaukar namiji ba ɗan goyo ba, ko kuma amincewa da zancen: ‘Duk wadda ta ɗauki Namiji Uba, tabbata za ta kwana marainiya.’ Kodayake sun fitar da nasu iyayen daga cikin lissafi saboda son kai da dabbanci da daƙiƙancin tunani irin na son kai.
Duk da wannan, akwai wasu mata da ƙaddara ce ta rayuwa ba fankama ko jahilci ya sanya suke kin namiji ba, wasu ma saboda wahalarvrayuwa da suka fuskanta a lokacin aure ko hulɗarsu; mussaman bayan sun fitar kutsu ta rayuwa. Sai dai hangen dala, ba shiga Kano ba.
Duk yadda matan bariki, ‘yan zamani da suke tinƙaho da Ilmi, wayewa ko kuɗi za su yi wa mazaje kuɗin goro; tabbata wasu daga cikinsu sunavda ɓoyayyun mazajen da ke yi musu hidima ko ta hulɗa ko ta aiki ko ma ta biyan buƙatunsu.
Wasu matan ma har girki suke yi suna kai wa wasu mazajen duk da irin cin fuskar da suke yi wa jinsinsu a hanyoyin sadarwa ko gabatar da ƙasidu a tarruruka.
Muhimmiyar shawara gare mu baki ɗaya, mu mutunta tare da girmama iyakokin juna, tare da tsare amana da gaskiya a kan zamantakewa tsakanin ma’aurata da ma hulɗa da juna.
Ba wata mace, mai lafiya da kuzari da za ta rayu babu namiji tare da ita; muddin har dai ta samu tarbiyya ta iyaye da kakanni.
Fata ɗaya da ya dace mu yi wa waɗanan matan, Allah Ya aza su a kan hanyar haƙuri da fahimtar addini da tarbiyya ta mutunci na rayuwa don kada su shiga wani mummunan yanayi na rayuwa.
~~~~~~~
Malam Yusuf Dingyadi, marubuci ne kuma ɗan jarida. Ya aiko muƙalar nan daga Sakkwato.
~~~~~~~













Sheguba kuma mune dawainiyarsu takomai ma Abu yana faruwa kanmu zasuyo