‘Yan Bindiga Sun Sako Miji Da Matarsa Bayan An Biya Naira Miliyan 50
Daga Wakilinmu

__________
A jiya Laraba da dare ne ‘yan bindiga da suka sace ɗan kasuwa a Katsina, Anas Ahmadu, tare da matarsa Halimatu mai juna biyu na watanni bakwai, da kuma ‘yarsu ‘yar shekara biyu, bayan sun biya Naira dubu 50 a matsayin kuɗin fansa, kamar yadda Jaridar Daily Trust ta ruwaito.
‘Yan bindigar sun sako su ne, bayan sun shafe makonni uku a hannunsu, in ji wani ɗan uwansu, wanda ya tabbatar da lamarin ga ‘yan jarida.
Ɗan uwan, wanda aka sakaya sunansa, ya bayyana cewa sai da suka biya kuɗin fansa na Naira miliyan 50, kafin masu garkuwar su sako masa ‘yan uwa.
“Alhamdulillah! Anas, Halimatu da ‘yarsu an sako su daga hannun masu garkuwa da su a daren nan. Suna kan hanyarsu zuwa gida. Amma an biya su kuɗin fansa na Naira miliyan 50,” in ji shi. Ya ƙara da cewa, saboda dalilan tsaro, ba za a bayyana inda aka karɓi waɗanda aka sace ba.
An sace magidantan ne a ranar 26 ga Agusta, 2025, inda aka ɗauke su daga gidansu da ke Unguwar Canada Quarters, cikin garin Katsina.
Da farko, masu garkuwar sun nemi kuɗin fansa na Naira miliyan 600, amma daga bisani suka rage zuwa miliyan 100 a ranar 3 ga Satumba, kafin a ƙarshe su amince da Naira miliyan 50.
_______













