TATTAUNAWAR KHALID IMAM: Zuwa Ga Malam Bashir
Daga Bukar Usman, OON
~~~~~~~
Da fatan lafiya da alheri.
Na karance doguwar tattaunawar da ka yi da Malam Khalid. Hirar ta yi kyau.
A gani na, ko da Malam Khalid ya bayyana cewa yadda wani gori da wata malamar makartarsu ta yi, shi ne ta sa shi da wasu ‘yan makarantarsu suka tashi haiƙan suka kama rubutu, da alamar ƙwarewar Malam Khalid a ɓangaren rubutu mai yawa; baiwa ce, tun da bai gaya mana wace makarantar koyon rubutu ta musamman da ya halarta ko wane marubuci ya koya masa rubuce-rubucen ba.
Dubi yawan littattafan zube da na ƙagaggu da na waƙoƙi da ya buga kuma bai tsaya a nan ba. Ba mu sani ba ko bakandamiyyarsa na nan tafe ba.
Fata na shi ne, Allah Ya ba shi tsawon rai da lafiya kuma Ya ƙarfafa masa gwiwa ta wajen rubutu da wasu sana’o’i da ya ce ya sa a gabansa.
Kuma yaransa guda biyu da ya ambata cewa suna bin sawunsa, Allah Ya sa su ci nasara kuma su ƙware wajen buƙatunsu da na mahaifa. Ba safai ba ne yara su gaji sana’ar iyaye, kamar yadda muka gani ga marigayi Mamman Shata. Kowa da irin baiwarsa.
Haza wassalam.
~~~~~~~
Dokta Bukar Usman, OON, fitaccen marubuci, masanin al’amuran tsaro kuma tsohon Babban-Sakatare a Fadar Shugaban Ƙasa, ya rubuto wannan wasiƙa ce bayan da ya karanta tattaunawar da aka yi da marubuci Khalid Imam, a Mujallar Taskar Gizago.
~~~~~~~














Mashaa Allah. Allah Ya qara ma rayuwa Albarka, Amin Ya Hayyu Ya Qayyum.
Amin Ya Allah. Muna matukar godiya.