Tunawa Da Umar Sa’idu Tudunwada
~~~~~~~
Baituka 11 domin ta’aziyyar
Gwarzon Ɗan Jarida, U.S.T.
Ya rasu ranar Lahadi 30-06-2019
27-Shawwal-1440 (BH)
~~~~~~~
Bawan Allah kai da kanka,
U.S.T. kai ne da kanka.
Za mu daɗe muna tuna ka,
Kullum jiddun kai da naka.
Na tuno ranar kai da kanka,
Shaida ka miƙan da kanka.
Alhamis ce ka zo da kanka,
Wajen taron kowa ya gan ka.
Iyan-Tama sun ce ka zo ka,
Babban baƙo ne kai da kanka.
2010 wannan ce shekararka,
Nuwamba shi ne watanka.
25 ce ranar ni dai na canka,
Shaidar ce ka ban da kanka.
Yau alhini muke rashin ka,
Alheri ka shuka kai da kanka.
Rediyon magana ne da kanka,
Ka koya ka koyar da kanka.
‘Yan uwa duka sun yaba ka
Kullum alheri ne nufin ka.
Allah Ka ji ƙan UST da kanKa,
Adana shi gidan nan Janna taKa
~~~~~~~
© Bashir Yahuza Malumfashi
~~~~~~~













