Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi ya jaddada wa al’ummar jiharsa cewa su kwantar da hankalinsu, domin ba za su yi nadamar zaben fa suka yi masa ba. Ya ce a shirye yake ya gudanar da ayyukan raya ƙasa a dukkan sassan jihar.
Gwamnan ya yi wannan batun ne a yayin bikin da aka shirya na taya murnar zaɓen Sanata mai wakiltar Arewa Maso Yamma ta Jihar Jigawa, Alhaji Babangida Hussaini, a ranar Asabar da ta gabata, a Kazaure.
“Ina ɗaukar maku alwashin cewa a Jihar Jigawa, tun daga kan Gwamna zuwa Sanatoci da ‘yan Majalisar Tarayya da na jiha, ba za mu ba ku kunya ba. Ba za ku yi nadamar zaɓen mu, a matsayin shugabanni ba. Za mu haɗa hannu mu yi maku aiki, domin kuwa bunƙasa Jihar Jigawa ne babban burinmu,” a cewar Gwamnan.
“Tun daga fara wannan tafiya, muka fitar da daftarin Ƙudurori-12 da muka raba wa al’umma cikin harsunan Ingilishi da Hausa. Za mu aiwatar da waɗannan ƙudurori na bunƙasa Jihar Jigawa. Don haka ina kira ga al’ummar jiha da su haɗa hannu da mu domin samun nasara.”
Gwamnan ya ce gwamnatinsa za ta ba gina matasa muhimmanci, domin kuwa su ne ƙashin bayan ci gaban jihar.
“Matasa su ne ƙashin bayan ci gabanmu. Bisa sakamakon ƙidayar jama’a ta gwaji da aka gudanar, Jihar Jigawa na da adadin mutane miliyan bakwai da rabi, inda a ciki, miliyan 3.2 duk matasa ne. Bisa ga haka, ba daidai ba ne a bar su a baya ba a jihar. Dalili ke nan ma ya sa muka kafa hukuma ta musamman da za ta kula da al’amuransu.”
Ya buƙaci al’ummar jihar da su riƙa ba da shawarwarin ci gaba ga gwamnati, a duk lokacin da suka ga buƙatar haka.
An dai tashi taron lafiya, wanda ya samu halartar manyan mutane daga sassa daban na ciki da wajen Jihar Jigawa, da suka haɗa da ‘yan majalisun tarayya da na jiha da jami’an gwamnati da sarakunan gargajiya da malaman addini.













