Matar Shugaban Ƙasa mai barin gado, Hajiya A’isha Muhammadu Buhari ta buƙaci gwamnatin ƙasar nan da ta yi sabon tsarin da za ta riƙa kula da rayuwar matan tsofaffin shugabannin ƙasa, kamar dai yadda take kula da su shugabannin da suka bar gadon mulki.
A’isha ta ce ya kamata a riƙa canja masu motocin shiga na alfarma, da daukar nauyin kula da lafiyarsu kuma a riƙa biyan su wasu kuɗaɗe na musamman, kamar dai yadda ake yi wa mazajensu, bayan sun bar gadon mulki.
Uwargidan Buhari ta faɗi haka ne a yayin bikin ƙaddamar da wani littafi a Abuja, wanda Shugabar Ƙungiyar Matan Manyan Jami’an Tsaro, Misis Vickie Anwuli Irabor ta rubuta, mai taken The Journey of a Military Wife.
“Mijina ya aure ni a matsayinsa na tsohon Shugaban Ƙasa kuma ga shi nan da ‘yan kwanaki biyu zan bar gidan gwamnati, bayan mijina ya yi mulki a matsayin Shugaban Ƙasa har zango biyu.
“Don haka ya kamata gwamnati ta kula da matan tsofaffin shugabannin ƙasa, a riƙa ba mu kulawa ta musamman da ta cancance mu, ba kawai kulawar ta riƙa tsayawa ga mazajenmu ba.” In ji A’isha Buhari, a yayin jawabinta.
Sai dai kuma masu sharhi kan al’amuran siyasa suna ganin irin wannan ɗawainiya ba ta dace ba. “Idan aka yi la’akari da tattalin arziƙin ƙasa da kuma cewa matan shugabannin ba zaɓen su aka yi ba, ɗawainiyar za ta yi wa gwamnati yawa kuma hakan zai haifar da sabuwar taƙaddama a tsakanin sauran matan gwamnoni da sauran ma’aikatan gwamnati,” in ji wani da ya buƙaci a sakaya sunansa.













